< 1 Chronicles 15 >

1 And he made him houses, in the city of David, —and prepared a place for the ark of God, and pitched for it a tent.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Then, said David, None must carry the ark of God, save the Levites, —for, of them, did Yahweh make choice, to bear the ark of Yahweh, and to attend it, unto times age-abiding.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 So David convoked all Israel, unto Jerusalem, —to bring up the ark of Yahweh, unto the place thereof, which he had prepared for it.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 And David gathered together the sons of Aaron, and the Levites:
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 Of the sons of Kohath, Uriel the chief, and his brethren, one hundred and twenty;
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 of the sons of Merari, Asaiah the chief, and his brethren, two hundred and twenty;
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 of the sons of Gershom, Joel the chief, and his brethren, one hundred and thirty;
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 of the sons of Elizaphan, Shemaiah the chief, and his brethren, two hundred;
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 of the sons of Hebron, Eliel the chief, and his brethren, eighty;
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 of the son of Uzziel, Amminadab the chief, and his brethren, a hundred and twelve.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 Then called David, for Zadok and for Abiathar, the priests, —and for the Levites, for Uriel, Asaiah and Joel, Shemaiah and Eliel, and Amminadab;
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 and said unto them, Ye, are the chiefs of the fathers of the Levites, —Hallow yourselves, ye and your brethren, so shall ye bring up the ark of Yahweh—God of Israel, into [the place] I have prepared for it.
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 Because, at the first, ye, did not [bring it], Yahweh our God brake forth against us, because we sought him not in the appointed way.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 So the priests and the Levites hallowed themselves, —to bring up the ark of Yahweh, God of Israel.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 And the sons of the Levites bare the ark of God, just as Moses commanded, according to the word of Yahweh, —on their shoulder, with the staves upon them.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 And David spake to the chiefs of the Levites, to station their brethren the singers, with instruments of song, harps and lyres, and cymbals, —sounding aloud at the lifting up of the voice, for joy.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 So the Levites caused to stand, Heman son of Joel, and, of his brethren, Asaph, son of Berechiah, —and, of the sons of Merari their brethren, Ethan, son of Kushaiah;
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 and, with them, their brethren of the second degree, —Zechariah, Ben, and Jaaziel, and Shemiramoth, and Jehiel and Unni, Eliab, and Benaiah, and Maaseiah, and Mattithiah, and Eliphelehu, and Mickneiah, and Obed-edom and Jeiel, the door-keepers.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 And, the singers, Heman, Asaph and Ethan, with cymbals of bronze, were to sound aloud;
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 and Zechariah, and Aziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, and Eliab, and Maaseiah and Benaiah, —with harps, over the trebles;
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 and Mattithiah, Eliphelehu, and Mikneiah, and Obed-edom, and Jeiel and Azaziah, —with lyres over the bass, to take the lead.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 And, Chenaniah the leader of the Levites, in the service, used to give instructions in the service, because skilful was he.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 And, Berechiah and Elkanah, were door-keepers to the ark.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 And, Shebaniah, and Joshaphat, and Nethanel, and Amasai, and Zechariah, and Benaiah, and Eliezer, the priests, were blowing with the trumpets, before the ark of God, —and, Obed-edom and Jehiah, were door-keepers, to the ark.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 Thus, it was, David and the elders of Israel, and the rulers of thousands, who were going, to bring up the ark of the covenant of Yahweh, out of the house of Obed-edom, with joy.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 And so it was that, when God helped the Levites, who were bearing the ark of the covenant of Yahweh, they sacrificed seven bullocks and seven rams.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 Now, David, was wrapped about with a robe of byssus, with all the Levites who were bearing the ark, and the singers, and Chenaniah the leader of the service rendered by the singers, —but, upon David, was an ephod of white linen.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 So, all Israel, were bringing up the ark of the covenant of Yahweh, with shouting, and with sound of the horn, and with trumpets, and with cymbals, —sounding aloud, with harps, and lyres.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 And so it was that, when the ark of the covenant of Yahweh came in as far as the city of David, —and Michal daughter of Saul looked forth through the window, and saw King David, dancing and playing, that she despised him in her heart.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.

< 1 Chronicles 15 >