< Psalms 99 >

1 The LORD reigneth; let the peoples tremble: he sitteth upon the cherubim; let the earth be moved.
Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
2 The LORD is great in Zion; and he is high above all the peoples.
Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
3 Let them praise thy great and terrible name: holy is he.
Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
4 The king’s strength also loveth judgment; thou dost establish equity, thou executest judgment and righteousness in Jacob.
Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
5 Exalt ye the LORD our God, and worship at his footstool: holy is he.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
6 Moses and Aaron among his priests, and Samuel among them that call on his name; they called upon the LORD, and he answered them.
Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
7 He spake unto them in the pillar of cloud: they kept his testimonies, and the statute that he gave them.
Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
8 Thou answeredst them, O LORD our God: thou wast a God that forgavest them, though thou tookest vengeance of their doings.
Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
9 Exalt ye the LORD our God, and worship at his holy hill; for the LORD our God is holy.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.

< Psalms 99 >