< Psalms 43 >

1 Judge me, O God, and plead my cause against an ungodly nation: O deliver me from the deceitful and unjust man.
Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
2 For thou art the God of my strength; why hast thou cast me off? why go I mourning because of the oppression of the enemy?
Kai ne Allah mafakata. Me ya sa ka ƙi ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?
3 O send out thy light and thy truth; let them lead me: let them bring me unto thy holy hill, and to thy tabernacles.
Ka aiko da haskenka da gaskiyarka, bari su bishe ni bari su kawo ni ga dutsenka mai tsarki, zuwa wurin da kake zama.
4 Then will I go unto the altar of God, unto God my exceeding joy: and upon the harp will I praise thee, O God, my God.
Sa’an nan zan tafi bagaden Allah, ga Allah, farin cikina da murnata. Zan yabe ka da garaya, Ya Allah, Allahna.
5 Why art thou cast down, O my soul? and why art thou disquieted within me? hope thou in God: for I shall yet praise him, [who is] the health of my countenance, and my God.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.

< Psalms 43 >