< Psalms 31 >

1 For the Chief Musician. A Psalm of David. In thee, O LORD, do I put my trust; let me never be ashamed: deliver me in thy righteousness.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
2 Bow down thine ear unto me; deliver me speedily: be thou to me a strong rock, an house of defence to save me.
Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 For thou art my rock and my fortress; therefore for thy name’s sake lead me and guide me.
Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 Pluck me out of the net that they have laid privily for me; for thou art my strong hold.
Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
5 Into thine hand I commend my spirit: thou hast redeemed me, O LORD, thou God of truth.
Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
6 I hate them that regard lying vanities: but I trust in the LORD.
Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
7 I will be glad and rejoice in thy mercy: for thou hast seen my affliction; thou hast known my soul in adversities:
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
8 And thou hast not shut me up into the hand of the enemy; thou hast set my feet in a large place.
Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
9 Have mercy upon me, O LORD, for I am in distress: mine eye wasteth away with grief, [yea], my soul and my body.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
10 For my life is spent with sorrow, and my years with sighing: my strength faileth because of mine iniquity, and my bones are wasted away.
Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
11 Because of all mine adversaries I am become a reproach, yea, unto my neighbours exceedingly, and a fear to mine acquaintance: they that did see me without fled from me.
Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
12 I am forgotten as a dead man out of mind: I am like a broken vessel.
An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
13 For I have heard the defaming of many, terror on every side: while they took counsel together against me, they devised to take away my life.
Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
14 But I trusted in thee, O LORD: I said, Thou art my God.
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15 My times are in thy hand: deliver me from the hand of mine enemies, and from them that persecute me.
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16 Make thy face to shine upon thy servant: save me in thy lovingkindness.
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17 Let me not he ashamed, O LORD; for I have called upon thee: let the wicked be ashamed, let them be silent in Sheol. (Sheol h7585)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
18 Let the lying lips be dumb; which speak against the righteous insolently, with pride and contempt.
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
19 Oh how great is thy goodness, which thou hast laid up for them that fear thee, which thou hast wrought for them that put their trust in thee, before the sons of men!
Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
20 In the covert of thy presence shalt thou hide them from the plottings of man: thou shalt keep them secretly in a pavilion from the strife of tongues.
Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
21 Blessed be the LORD: for he hath shewed me his marvelous lovingkindness in a strong city.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
22 As for me, I said in my haste, I am cut off from before thine eyes: nevertheless thou heardest the voice of my supplications when I cried unto thee.
Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
23 O love the LORD, all ye his saints: the LORD preserveth the faithful, and plentifully rewardeth the proud doer.
Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
24 Be strong, and let your heart take courage, all ye that hope in the LORD.
Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.

< Psalms 31 >