< Proverbs 28 >

1 The wicked flee when no man pursueth: but the righteous are bold as a lion.
Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
2 For the transgression of a land many are the princes thereof: but by men of understanding [and] knowledge the state [thereof] shall be prolonged.
Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
3 A needy man that oppresseth the poor is [like] a sweeping rain which leaveth no food.
Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
4 They that forsake the law praise the wicked: but such as keep the law contend with them.
Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
5 Evil men understand not judgment: but they that seek the LORD understand all things.
Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
6 Better is the poor that walketh in his integrity, than he that is perverse in [his] ways, though he be rich.
Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
7 Whoso keepeth the law is a wise son: but he that is a companion of gluttonous men shameth his father.
Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
8 He that augmenteth his substance by usury and increase, gathereth it for him that hath pity on the poor.
Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
9 He that turneth away his ear from hearing the law, even his prayer is an abomination.
In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
10 Whoso causeth the upright to go astray in an evil way, he shall fall himself into his own pit: but the perfect shall inherit good.
Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
11 The rich man is wise in his own conceit; but the poor that hath understanding searcheth him out.
Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
12 When the righteous triumph, there is great glory: but when the wicked rise, men hide themselves.
Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
13 He that covereth his transgressions shall not prosper: but whoso confesseth and forsaketh them shall obtain mercy.
Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
14 Happy is the man that feareth alway: but he that hardeneth his heart shall fall into mischief.
Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
15 [As] a roaring lion, and a ranging bear; [so is] a wicked ruler over a poor people.
Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
16 The prince that lacketh understanding is also a great oppressor: [but] he that hateth covetousness shall prolong his days.
Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
17 A man that is laden with the blood of any person shall flee unto the pit; let no man stay him.
Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
18 Whoso walketh uprightly shall be delivered: but he that is perverse in [his] ways shall fall at once.
Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
19 He that tilleth his land shall have plenty of bread: but he that followeth after vain [persons] shall have poverty enough.
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
20 A faithful man shall abound with blessings: but he that maketh haste to be rich shall not be unpunished.
Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
21 To have respect of persons is not good: neither that a man should transgress for a piece of bread.
Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
22 He that hath an evil eye hasteth after riches, and knoweth not that want shall come upon him.
Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
23 He that rebuketh a man shall afterward find more favour than he that flattereth with the tongue.
Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
24 Whoso robbeth his father or his mother, and saith, It is no transgression; the same is the companion of a destroyer.
Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
25 He that is of a greedy spirit stirreth up strife: but he that putteth his trust in the LORD shall be made fat.
Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
26 He that trusteth in his own heart is a fool: but whoso walketh wisely, he shall be delivered.
Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
27 He that giveth unto the poor shall not lack: but he that hideth his eyes shall have many a curse.
Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
28 When the wicked rise, men hide themselves: but when they perish, the righteous increase.
Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.

< Proverbs 28 >