< Obadiah 1 >

1 The vision of Obadiah. Thus saith the Lord GOD concerning Edom: We have heard tidings from the LORD, and an ambassador is sent among the nations, [saying], Arise ye, and let us rise up against her in battle.
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Behold, I have made thee small among the nations: thou art greatly despised.
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 The pride of thine heart hath deceived thee, O thou that dwellest in the clefts of the rock, whose habitation is high; that saith in his heart, Who shall bring me down to the ground?
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 Though thou mount on high as the eagle, and though thy nest be set among the stars, I will bring thee down from thence, saith the LORD.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 If thieves came to thee, if robbers by night, (how art thou cut off!) would they not steal till they had enough? if grapegatherers came to thee, would they not leave some gleaning grapes?
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 How are [the things of] Esau searched out! how are his hidden treasures sought up!
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 All the men of thy confederacy have brought thee on thy way, even to the border: the men that were at peace with thee have deceived thee, and prevailed against thee; [they that eat] thy bread lay a snare under thee: there is none understanding in him.
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 Shall I not in that day, saith the LORD, destroy the wise men out of Edom, and understanding out of the mount of Esau?
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 And thy mighty men, O Teman, shall be dismayed, to the end that every one may be cut off from the mount of Esau by slaughter.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 For the violence done to thy brother Jacob shame shall cover thee, and thou shalt be cut off for ever.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 In the day that thou stoodest on the other side, in the day that strangers carried away his substance, and foreigners entered into his gates, and cast lots upon Jerusalem, even thou wast as one of them.
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 But look not thou on the day of thy brother in the day of his disaster, and rejoice not over the children of Judah in the day of their destruction; neither speak proudly in the day of distress.
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 Enter not into the gate of my people in the day of their calamity; yea, look not thou on their affliction in the day of their calamity, neither lay ye [hands] on their substance in the day of their calamity.
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 And stand thou not in the crossway, to cut off those of his that escape; and deliver not up those of his that remain in the day of distress.
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 For the day of the LORD is near upon all the nations: as thou hast done, it shall be done unto thee; thy dealing shall return upon thine own head.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 For as ye have drunk upon my holy mountain, so shall all the nations drink continually, yea, they shall drink, and swallow down, and shall be as though they had not been.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 But in mount Zion there shall be those that escape, and it shall be holy; and the house of Jacob shall possess their possessions.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 And the house of Jacob shall be a fire, and the house of Joseph a flame, and the house of Esau for stubble, and they shall burn among them, and devour them: and there shall not be any remaining to the house of Esau; for the LORD hath spoken it.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 And they of the South shall possess the mount of Esau; and they of the lowland the Philistines and they shall possess the field of Ephraim, and the field of Samaria: and Benjamin [shall possess] Gilead.
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 And the captivity of this host of the children of Israel, which are [among] the Canaanites, [shall possess] even unto Zarephath; and the captivity of Jerusalem, which is in Sepharad, shall possess the cities of the South.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 And saviours shall come up on mount Zion to judge the mount of Esau; and the kingdom shall be the LORD’S.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Obadiah 1 >