< Numbers 1 >

1 And the LORD spake unto Moses in the wilderness of Sinai, in the tent of meeting, on the first day of the second month, in the second year after they were come out of the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Take ye the sum of all the congregation of the children of Israel, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, every male, by their polls;
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 from twenty years old and upward, all that are able to go forth to war in Israel, thou and Aaron shall number them by their hosts.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And with you there shall be a man of every tribe; every one head of his fathers’ house.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 And these are the names of the men that shall stand with you: of Reuben; Elizur the son of Shedeur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Of Simeon; Shelumiel the son of Zurishaddai.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Of Judah; Nahshon the son of Amminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Of Issachar; Nethanel the son of Zuar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Of Zebulun; Eliab the son of Helon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Of the children of Joseph: of Ephraim; Elishama the son of Ammihud: of Manasseh; Gamaliel the son of Pedahzur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Of Benjamin; Abidan the son of Gideoni.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Of Dan; Ahiezer the son of Ammishaddai.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Of Asher; Pagiel the son of Ochran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Of Gad; Eliasaph the son of Deuel.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Of Naphtali; Ahira the son of Enan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These are they that were called of the congregation, the princes of the tribes of their fathers; they were the heads of the thousands of Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 And Moses and Aaron took these men which are expressed by name:
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And they assembled all the congregation together on the first day of the second month, and they declared their pedigrees after their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, by their polls.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 As the LORD commanded Moses, so he numbered them in the wilderness of Sinai.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 And the children of Reuben, Israel’s firstborn, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, by their polls, every male from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 those that were numbered of them, of the tribe of Reuben, were forty and six thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Of the children of Simeon, their generations, by their families, by their fathers’ houses, those that were numbered thereof, according to the number of the names, by their polls, every male from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 those that were numbered of them, of the tribe of Simeon, were fifty and nine thousand and three hundred.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Of the children of Gad, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 those that were numbered of them, of the tribe of Gad, were forty and five thousand six hundred and fifty.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Of the children of Judah, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 those that were numbered of them, of the tribe of Judah, were threescore and fourteen thousand and six hundred.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Of the children of Issachar, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 those that were numbered of them, of the tribe of Issachar, were fifty and four thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Of the children of Zebulun, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 those that were numbered of them, of the tribe of Zebulun, were fifty and seven thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Of the children of Joseph, [namely], of the children of Ephraim, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 those that were numbered of them, of the tribe of Ephraim, were forty thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Of the children of Manasseh, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 those that were numbered of them, of the tribe of Manasseh, were thirty and two thousand and two hundred.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Of the children of Benjamin, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 those that were numbered of them, of the tribe of Benjamin, were thirty and five thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Of the children of Dan, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 those that were numbered of them, of the tribe of Dan, were threescore and two thousand and seven hundred.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Of the children of Asher, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 those that were numbered of them, of the tribe of Asher, were forty and one thousand and five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Of the children of Naphtali, their generations, by their families, by their fathers’ houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war;
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 those that were numbered of them, of the tribe of Naphtali, were fifty and three thousand and four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These are they that were numbered, which Moses and Aaron numbered, and the princes of Israel, being twelve men: they were each one for his fathers’ house.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 So all they that were numbered of the children of Israel by their fathers’ houses, from twenty years old and upward, all that were able to go forth to war in Israel;
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 even all they that were numbered were six hundred thousand and three thousand and five hundred and fifty.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Levites after the tribe of their fathers were not numbered among them.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 For the LORD spake unto Moses, saying,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Only the tribe of Levi thou shalt not number, neither shalt thou take the sum of them among the children of Israel:
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 but appoint thou the Levites over the tabernacle of the testimony, and over all the furniture thereof, and over all that belongeth to it: they shall bear the tabernacle, and all the furniture thereof; and they shall minister unto it, and shall encamp round about the tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 And when the tabernacle setteth forward, the Levites shall take it down: and when the tabernacle is to be pitched, the Levites shall set it up: and the stranger that cometh nigh shall be put to death.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 And the children of Israel shall pitch their tents, every man by his own camp, and every man by his own standard, according to their hosts.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But the Levites shall pitch round about the tabernacle of the testimony, that there be no wrath upon the congregation of the children of Israel: and the Levites shall keep the charge of the tabernacle of the testimony.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Thus did the children of Israel; according to all that the LORD commanded Moses, so did they.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >