< Judges 1 >

1 And it came to pass after the death of Joshua, that the children of Israel asked of the LORD, saying, Who shall go up for us first against the Canaanites, to fight against them?
Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
2 And the LORD said, Judah shall go up: behold, I have delivered the land into his hand.
Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
3 And Judah said unto Simeon his brother, Come up with me into my lot, that we may fight against the Canaanites; and I likewise will go with thee into thy lot. So Simeon went with him.
Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
4 And Judah went up; and the LORD delivered the Canaanites and the Perizzites into their hand: and they smote of them in Bezek ten thousand men.
Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
5 And they found Adoni-bezek in Bezek: and they fought against him, and they smote the Canaanites and the Perizzites.
A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
6 But Adoni-bezek fled; and they pursued after him, and caught him, and cut off his thumbs and his great toes.
Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
7 And Adoni-bezek said, Threescore and ten kings, having their thumbs and their great toes cut off, gathered [their meat] under my table: as I have done, so God hath requited me. And they brought him to Jerusalem, and he died there.
Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
8 And the children of Judah fought against Jerusalem, and took it, and smote it with the edge of the sword, and set the city on fire.
Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
9 And afterward the children of Judah went down to fight against the Canaanites that dwelt in the hill country, and in the South, and in the lowland.
Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
10 And Judah went against the Canaanites that dwelt in Hebron: (now the name of Hebron beforetime was Kiriath-arba: ) and they smote Sheshai, and Ahiman, and Talmai.
Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
11 And from thence he went against the inhabitants of Debir. (Now the name of Debir beforetime was Kiriath-sepher.)
Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
12 And Caleb said, He that smiteth Kiriath-sepher, and taketh it, to him will I give Achsah my daughter to wife.
Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
13 And Othniel the son of Kenaz, Caleb’s younger brother, took it: and he gave him Achsah his daughter to wife.
Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
14 And it came to pass, when she came [unto him], that she moved him to ask of her father a field: and she lighted down from off her ass; and Caleb said unto her, What wouldest thou?
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
15 And she said unto him, Give me a blessing; for that thou hast set me in the land of the South, give me also springs of water. And Caleb gave her the upper springs and the nether springs.
Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
16 And the children of the Kenite, Moses’ brother in law, went up out of the city of palm trees with the children of Judah into the wilderness of Judah, which is in the south of Arad; and they went and dwelt with the people.
Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
17 And Judah went with Simeon his brother, and they smote the Canaanites that inhabited Zephath, and utterly destroyed it. And the name of the city was called Hormah.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
18 Also Judah took Gaza with the border thereof, and Ashkelon with the border thereof, and Ekron with the border thereof.
Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
19 And the LORD was with Judah; and he drave out [the inhabitants of] the hill country; for he could not drive out the inhabitants of the valley, because they had chariots of iron.
Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
20 And they gave Hebron unto Caleb, as Moses had spoken: and he drave out thence the three sons of Anak.
Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
21 And the children of Benjamin did not drive out the Jebusites that inhabited Jerusalem: but the Jebusites dwelt with the children of Benjamin in Jerusalem, unto this day.
Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
22 And the house of Joseph, they also went up against Beth-el: and the LORD was with them.
To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
23 And the house of Joseph sent to spy out Beth-el. (Now the name of the city beforetime was Luz.)
Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
24 And the watchers saw a man come forth out of the city, and they said unto him, Shew us, we pray thee, the entrance into the city, and we will deal kindly with thee.
’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
25 And he shewed them the entrance into the city, and they smote the city with the edge of the sword; but they let the man go and all his family.
Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
26 And the man went into the land of the Hittites, and built a city, and called the name thereof Luz: which is the name thereof unto this day.
Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
27 And Manasseh did not drive out [the inhabitants of] Beth-shean and her towns, nor [of] Taanach and her towns, nor the inhabitants of Dor and her towns, nor the inhabitants of Ibleam and her towns, nor the inhabitants of Megiddo and her towns: but the Canaanites would dwell in that land.
Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
28 And it came to pass, when Israel was waxen strong, that they put the Canaanites to taskwork, and did not utterly drive them out.
Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
29 And Ephraim drave not out the Canaanites that dwelt in Gezer; but the Canaanites dwelt in Gezer among them.
Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
30 Zebulun drave not out the inhabitants of Kitron, nor the inhabitants of Nahalol; but the Canaanites dwelt among them, and became tributary.
Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
31 Asher drave not out the inhabitants of Acco, nor the inhabitants of Zidon, nor of Ahlab, nor of Achzib, nor of Helbah, nor of Aphik, nor of Rehob:
Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
32 but the Asherites dwelt among the Canaanites, the inhabitants of the land: for they did not drive them out.
kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
33 Naphtali drave not out the inhabitants of Beth-shemesh, nor the inhabitants of Beth-anath; but he dwelt among the Canaanites, the inhabitants of the land: nevertheless the inhabitants of Beth-shemesh and of Beth-anath became tributary unto them.
Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
34 And the Amorites forced the children of Dan into the hill country: for they would not suffer them to come down to the valley:
Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
35 but the Amorites would dwell in mount Heres, in Aijalon, and in Shaalbim: yet the hand of the house of Joseph prevailed, so that they became tributary.
Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
36 And the border of the Amorites was from the ascent of Akrabbim, from the rock, and upward.
Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.

< Judges 1 >