< Exodus 21 >

1 Now these are the judgments which thou shalt set before them.
“Waɗannan su ne dokokin da za ka sa a gabansu.
2 If thou buy an Hebrew servant, six years he shall serve: and in the seventh he shall go out free for nothing.
“In ka sayi mutumin Ibraniyawa a matsayin bawa, zai bauta maka shekara shida. Amma a shekara ta bakwai, za ka’yantar da shi, yă tafi’yantacce, ba tare da ya biya kome ba.
3 If he come in by himself, he shall go out by himself: if he be married, then his wife shall go out with him.
In ya zo shi kaɗai, zai tafi’yantacce shi kaɗai; amma in yana da mata a lokacin da ya zo, za tă tafi tare da shi.
4 If his master give him a wife, and she bear him sons or daughters; the wife and her children shall be her master’s, and he shall go out by himself.
In maigidansa ya yi masa aure, ta kuwa haifa masa’ya’ya maza ko mata, matan da’ya’yan, za su zama na maigidan, sai mutumin kaɗai zai tafi’yantacce.
5 But if the servant shall plainly say, I love my master, my wife, and my children; I will not go out free:
“Amma in bawan ya furta ya ce, ‘Ina ƙaunar maigidana, da matata, da’ya’yana, ba na so kuma in’yantu,’
6 then his master shall bring him unto God, and shall bring him to the door, or unto the door post; and his master shall bore his ear through with an awl; and he shall serve him for ever.
dole maigidansa yă kai shi gaban alƙalai. Zai kai shi ƙofa ko madogarar ƙofa, yă huda kunnensa da basilla, sa’an nan zai zama bawansa duk tsawon kwanakinsa a duniya.
7 And if a man sell his daughter to be a maidservant, she shall not go out as the menservants do.
“In mutum ya sayar da’yarsa a matsayin baiwa, ba za a’yantar da ita kamar bawa ba.
8 If she please not her master, who hath espoused her to himself, then shall he let her be redeemed: to sell her unto a strange people he shall have no power, seeing he hath dealt deceitfully with her.
In ba tă gamshi maigida wanda ya zaɓe ta domin kansa ba, dole yă bari a fanshe ta. Ba shi da dama yă sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba.
9 And if he espouse her unto his son, he shall deal with her after the manner of daughters.
In ya zaɓe ta domin ɗansa, dole yă ba ta duk damar da’ya ta mace take da shi.
10 If he take him another [wife]; her food, her raiment, and her duty of marriage, shall he not diminish.
In ya auri wata mace, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba.
11 And if he do not these three unto her, then shall she go out for nothing, without money.
In bai tanada mata waɗannan abubuwa uku ba, sai tă tafi’yantacciya, babu biyan kome.
12 He that smiteth a man, so that he die, shall surely be put to death.
“Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle a kashe shi.
13 And if a man lie not in wait, but God deliver [him] into his hand; then I will appoint thee a place whither he shall flee.
Amma in ba da nufin yă kashe shi ba, sai dai in Allah ne ya nufa haka, to, sai mutumin yă tsere zuwa inda zan nuna muku.
14 And if a man come presumptuously upon his neighbour, to slay him with guile; thou shalt take him from mine altar, that he may die.
Amma in mutumin ya yi dabara har ya kashe wani mutum da gangan, sai a ɗauke shi daga bagadena a kashe shi.
15 And he that smiteth his father, or his mother, shall be surely put to death.
“Duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
16 And he that stealeth a man, and selleth him, or if he be found in his hand, he shall surely be put to death.
“Duk wanda ya saci mutum ya sayar da shi, ko kuwa aka iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.
17 And he that curseth his father, or his mother, shall surely be put to death.
“Duk wanda ya la’anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
18 And if men contend, and one smiteth the other with a stone, or with his fist, and he die not, but keep his bed:
“Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,
19 if he rise again, and walk abroad upon his staff, then shall he that smote him be quit: only he shall pay for the loss of his time, and shall cause him to be thoroughly healed.
idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda ne, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓata masa, yă kuma lura da shi, har yă warke sarai.
20 And if a man smite his servant, or his maid, with a rod, and he die under his hand; he shall surely be punished.
“In mutum ya dūke bawansa ko baiwarsa da sanda, sai bawan ko baiwar ta mutu saboda dūkan, dole a hukunta shi,
21 Notwithstanding, if he continue a day or two, he shall not be punished: for he is his money.
amma ba za a hukunta shi ba, in bawan ko baiwar ta tashi, bayan kwana ɗaya ko biyu, tun da bawan ko baiwar mallakarsa ne.
22 And if men strive together, and hurt a woman with child, so that her fruit depart, and yet no mischief follow: he shall be surely fined, according as the woman’s husband shall lay upon him; and he shall pay as the judges determine.
“Idan mutum biyu suna faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka za a biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.
23 But if any mischief follow, then thou shalt give life for life,
Amma in akwai rauni mai tsanani, sai a ɗauki rai a maimakon rai,
24 eye for eye, tooth for tooth, hand for hand, foot for foot,
ido don ido, haƙori don haƙori, hannu don hannu, ƙafa don ƙafa,
25 burning for burning, wound for wound, stripe for stripe.
ƙuna don ƙuna, rauni don rauni, ƙujewa don ƙujewa.
26 And if a man smite the eye of his servant, or the eye of his maid, and destroy it; he shall let him go free for his eye’s sake.
“In mutum ya bugi bawa ko baiwa a ido, har idon ya lalace, dole yă’yantar da shi ko ita, maimakon ido.
27 And if he smite out his manservant’s tooth, or his maidservant’s tooth; he shall let him go free for his tooth’s sake.
In kuma ya fangare haƙorin bawa ko baiwa, dole yă’yantar da bawan ko baiwar, a maimakon haƙorin.
28 And if an ox gore a man or a woman, that they die, the ox shall be surely stoned, and his flesh shall not be eaten; but the owner of the ox shall be quit.
“In bijimi ya kashe namiji ko ta mace, dole a jajjefe bijimin har yă mutu, ba za a kuma ci namansa ba. Amma mai bijimin ba shi da laifi.
29 But if the ox were wont to gore in time past, and it hath been testified to his owner, and he hath not kept him in, but that he hath killed a man or a woman; the ox shall be stoned, and his owner also shall be put to death.
In, har an san bijimin da wannan hali, an kuma yi wa mai shi gargaɗi, amma bai ɗaura shi ba, har ya kashe namiji ko ta mace, za a jajjefe bijimin tare da mai shi, har su mutu.
30 If there be laid on him a ransom, then he shall give for the redemption of his life whatsoever is laid upon him.
Amma fa, in an bukace shi yă biya, zai biya don yă fanshi ransa ta wurin biyan abin da aka aza masa.
31 Whether he have gored a son, or have gored a daughter, according to this judgment shall it be done unto him.
Wannan doka ta shafi batun bijimin da ya kashe ɗa ko’ya.
32 If the ox gore a manservant or a maidservant; he shall give unto their master thirty shekels of silver, and the ox shall be stoned.
In bijimin ya kashe bawa ko baiwa, mai shi zai biya shekel talatin na azurfa wa maigidan bawan, a kuma a jajjefe bijimin.
33 And if a man shall open a pit, or if a man shall dig a pit and not cover it, and an ox or an ass fall therein,
“In mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai kuma rufe ba, sai saniya ko jaki ya fāɗi a ciki,
34 the owner of the pit shall make it good; he shall give money unto the owner of them, and the dead [beast] shall be his.
Mai ramin zai biya rashin da aka yi wa mai shi, matacciyar saniyan ko jakin, zai zama na mai ramin.
35 And if one man’s ox hurt another’s, that he die; then they shall sell the live ox, and divide the price of it; and the dead also they shall divide.
“In bijimin mutum ya raunana bijimin wani, har ya mutu, sai mutanen biyu su sayar da mai ran, su raba kuɗin daidai, haka ma su yi da mai ran.
36 Or if it be known that the ox was wont to gore in time past, and his owner hath not kept him in; he shall surely pay ox for ox, and the dead [beast] shall be his own.
Amma fa, in tun can, an san bijimin yana da wannan halin faɗa, duk da haka mai shi bai ɗaura shi ba, dole mai shi yă biya, dabba domin dabba, matacciyar dabbar kuwa tă zama nasa.

< Exodus 21 >