< Luke 5 >

1 Once, when the people were pressing around Jesus as they listened to God’s message, he happened to be standing by the shore of the Lake of Gennesaret, and saw two boats close to the shore.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 The fishermen had gone away from them and were washing the nets.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 So, getting into one of the boats, which belonged to Simon, Jesus asked him to push off a little way from the shore, and then sat down and taught the people from the boat.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 When he had finished speaking, he said to Simon, “Push off into deep water, and throw out your nets for a haul.”
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 “We have been hard at work all night, Sir,” answered Simon, “and have not caught anything, but, at your bidding, I will throw out the nets.”
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 They did so, and enclosed such a great shoal of fish that their nets began to break.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 So they signaled to their partners in the other boat to come and help them; and they came and filled both the boats so full of fish that they were almost sinking.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 When Simon Peter saw this, he threw himself down at Jesus’ knees, exclaiming, “Master, leave me, for I am a sinful man!”
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For he and all who were with him were lost in amazement at the haul of fish which they had made;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 and so, too, were James and John, Zebedee’s sons, who were Simon’s partners. “Do not be afraid,” Jesus said to Simon, “from today you will catch people.”
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 And, when they had brought their boats to shore, they left everything, and followed him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 On one occasion Jesus was staying in a town, when he saw a man who was covered with leprosy. When the leper saw Jesus, he threw himself on his face and implored his help, “Master, if only you are willing, you are able to make me clean.”
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Stretching out his hand, Jesus touched him, saying as he did so, “I am willing; become clean.” Instantly the leprosy left the man;
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 and then Jesus impressed on him that he was not to say a word to anyone, “but,” he added, “set out and show yourself to the priest, and make the offerings for your cleansing, in the manner directed by Moses, as evidence of your cure.”
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 However, the story about Jesus spread all the more, and great crowds came together to listen to him, and to be cured of their illnesses;
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 but Jesus used to withdraw to lonely places and pray.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 On one of those days, when Jesus was teaching, some Pharisees and Doctors of the Law were sitting near by. (They had come from all the villages in Galilee and Judea, and from Jerusalem; and the power of the Lord was on Jesus, so that he could work cures.)
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 And there some men brought on a bed a man who was paralyzed. They tried to get him in and lay him before Jesus;
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 but, finding no way of getting him in owing to the crowd, they went up on the roof and lowered him through the tiles, with his pallet, into the middle of the people and in front of Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 When he saw their faith, Jesus said, “Friend, your sins have been forgiven you.”
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 The teachers of the Law and the Pharisees began debating about this. “Who is this man who speaks so blasphemously?” they asked. “Who can forgive sins except God?”
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 When Jesus became aware of the way in which they were debating, he turned to them and exclaimed, “What are you debating with yourselves?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Which is the easier? – to say ‘Your sins have been forgiven you’? Or to say ‘Get up, and walk’?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But so that you may know that the Son of Man has power on earth to forgive sins” – he spoke to the paralyzed man – “To you I say, Get up, and take up your pallet, and go to your home.”
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Instantly the man stood up before their eyes, took up what he had been lying on, and went to his home, praising God.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 The people, one and all, were lost in amazement, and praised God; and in great awe they said, “We have seen marvelous things today!”
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 After this, Jesus went out; and he noticed a tax-gatherer, named Levi, sitting in the tax office, and said to him, “Follow me.”
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Levi left everything and got up and followed him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 And Levi gave a great banquet at his house, in honor of Jesus; and a large number of tax collectors and others were having dinner with them.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 The Pharisees and the teachers of the Law belonging to their party complained of this to the disciples of Jesus.
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 In answer Jesus said, “It is not those who are well who need a doctor, but those who are ill.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I have not come to call the religious, but the outcast, to repent.”
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 “John’s disciples,” they said to Jesus, “Often fast and say prayers, and so do the disciples of the Pharisees, while yours are eating and drinking!”
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 But Jesus answered them, “Can you make the groom’s friends fast while the groom is with them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But the days will come – a time when the groom will be taken away from them; and they will fast then, when those days come.”
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Then, as an illustration, Jesus said to them, “No one ever tears a piece from a new garment and puts it on an old one; for, if they do, they will not only tear the new garment, but the piece from the new one will not match the old.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 And no one puts new wine into old wine-skins; for, if they do, the new wine will burst the skins, and the wine itself will run out, and the skins be lost.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But new wine must be put into fresh skins.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 No one after drinking old wine wishes for new. ‘No,’ they say, ‘the old is excellent.’”
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >