< Luke 18 >

1 Jesus told his disciples a parable to show them that they should always pray and never despair.
Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
2 “There was,” he said, “in a certain town a judge, who had no fear of God nor regard for people.
yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
3 In the same town there was a widow who went to him again and again, and said ‘Grant me justice against my opponent.’
Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
4 For a time the judge refused, but afterward he said to himself ‘Although I am without fear of God or regard for people,
An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
5 yet, as this widow is so troublesome, I will grant her justice, to stop her from plaguing me with her endless visits.’”
duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
6 Then the Master added, “Listen to what this iniquitous judge says!
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
7 And God – won’t he see that his own people, who cry to him night and day, have justice done them – though he holds his hand?
A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
8 He will, I tell you, give them justice soon enough! Yet, when the Son of Man comes, will he find faith on earth?”
Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
9 Another time, speaking to people who were satisfied that they were religious, and who regarded everyone else with scorn, Jesus told this parable –
Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
10 “Two men went up into the Temple Courts to pray. One was a Pharisee and the other a tax-gatherer.
“Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
11 The Pharisee stood forward and began praying to himself in this way – ‘God, I thank you that I am not like other men – thieves, rogues, adulterers – or even like this tax-gatherer.
Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
12 I fast twice a week, and give a tenth of everything I get to God.’
Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
13 Meanwhile the tax-gatherer stood at a distance, not venturing even to raise his eyes to heaven, but he kept striking his breast and saying ‘God, have mercy on me, a sinner.’
Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
14 This man, I tell you, went home pardoned, rather than the other. For everyone who exalts himself will be humbled, while everyone who humbles himself will be exalted.”
Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
15 Some of the people were bringing even their babies to Jesus, for him to touch them; but, when the disciples saw it, they began to find fault with those who had brought them.
Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
16 Jesus, however, called the little children to him. “Let the little children come to me,” he said, “and do not hinder them, for it is to the childlike that the kingdom of God belongs.
Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
17 I tell you, unless a man receives the kingdom of God like a child, he will not enter it at all.”
Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
18 And one of the leaders asked Jesus this question – “Good teacher, what must I do if I am to gain eternal life?” (aiōnios g166)
Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
19 “Why do you call me good?” answered Jesus. “No one is good but God.
Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
20 You know the commandments – Do not commit adultery, Do not kill, Do not steal, Do not say what is false about others, Honor your father and your mother.”
Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
21 “I have observed all these,” he replied, “from childhood.”
Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
22 Hearing this, Jesus said to him, “There is one thing still lacking in you; sell everything that you have, and distribute to the poor, and you will have wealth in heaven; then come and follow me.”
Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
23 But the man became greatly distressed on hearing this, for he was extremely rich.
Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
24 Seeing this, Jesus said to his disciples, “How hard it is for the wealthy to enter the kingdom of God!
Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
25 It is easier, indeed, for a camel to get through a needle’s eye than for a rich person to enter the kingdom of God!”
Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 “Then who can be saved?” asked those who heard this.
Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
27 But Jesus said, “What is impossible with people is possible with God.”
Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28 “But we,” said Peter, “we left what belonged to us and followed you.”
Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29 “I tell you,” he answered, “that there is no one who has left house, or wife, or brothers, or parents, or children, for the sake of the kingdom of God,
Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
30 who will not receive many times as much in the present, and in the age that is coming eternal life.” (aiōn g165, aiōnios g166)
sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Gathering the Twelve around him, Jesus said to them, “Listen! We are going up to Jerusalem; and there everything that is written in the prophets will be done to the Son of Man.
Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
32 For he will be given up to the Gentiles, mocked, insulted and spat on;
Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
33 they will scourge him, and then put him to death; and on the third day he will rise again.”
Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
34 The apostles did not comprehend any of this. His meaning was unintelligible to them and they did not understand what he was saying.
Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35 As Jesus was getting near Jericho, a blind man was sitting by the roadside, begging.
Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
36 Hearing a crowd going by, the man asked what was the matter;
da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
37 and, when people told him that Jesus of Nazareth was passing,
Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
38 he shouted out, “Jesus, Son of David, take pity on me!”
Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
39 Those who were in front kept telling him to be quiet, but he continued to call out the louder, “Son of David, take pity on me!”
Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
40 Then Jesus stopped and ordered the man to be brought to him. And, when he had come close up to him, Jesus asked him,
Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
41 “What do you want me to do for you?” “Master,” he said, “I want to recover my sight.”
“Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
42 And Jesus said, “Recover your sight, your faith has delivered you.”
Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 Instantly he recovered his sight, and began to follow Jesus, praising God. And all the people, on seeing it, gave glory to God.
Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.

< Luke 18 >