< Luke 1 >

1 To his Excellency, Theophilus. Many attempts have been already made to draw up an account of those events which have reached their conclusion among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 just as they were reported to us by those who from the beginning were eye-witnesses, and afterward became bearers of the message.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 And, therefore, I also, since I have investigated all these events with great care from their very beginning, have resolved to write a connected history of them for you,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 in order that you may be able to satisfy yourself of the accuracy of the story which you have heard from the lips of others.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the reign of Herod, king of Judea, there was a priest named Zechariah, who belonged to the division called after Abijah. His wife, whose name was Elizabeth, was also a descendant of Aaron.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both righteous people, who lived blameless lives, guiding their steps by all the commandments and ordinances of the Lord.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no child, Elizabeth being barren; and both of them were advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 One day, when Zechariah was officiating as priest before God, during the turn of his division,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 it fell to him by lot, in accordance with the practice among the priests, to go into the Temple of the Lord and burn incense;
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and, as it was the Hour of Incense, the people were all praying outside.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And an angel of the Lord appeared to him, standing on the right of the Altar of Incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zechariah was startled at the sight and was awe-struck.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah; your prayer has been heard, and your wife Elizabeth will bear you a son, whom you will call by the name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 He will be to you a joy and a delight; and many will rejoice over his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord; he will not drink any wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth,
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 and will reconcile many of the Israelites to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 He will go before him in the spirit and with the power of Elijah, to reconcile fathers to their children and the disobedient to the wisdom of the righteous, and so make ready for the Lord a people prepared for him.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 “How can I be sure of this?” Zechariah asked the angel. “For I am an old man and my wife is advanced in years.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 “I am Gabriel,” the angel answered, “who stand in the presence of God, and I have been sent to speak to you and to bring you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And now you will be silent and unable to speak until the day when this takes place, because you did not believe what I said, though my words will be fulfilled in due course.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Meanwhile the people were watching for Zechariah, wondering at his remaining so long in the Temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 When he came out, he was unable to speak to them, and they perceived that he had seen a vision there. But Zechariah kept making signs to them, and remained dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And, as soon as his term of service was finished, he returned home.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 After this his wife, Elizabeth, became pregnant and lived in seclusion for five months.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “The Lord has done this for me,” she said, “he has shown me kindness and taken away the public disgrace of childlessness under which I have been living.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Six months later the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a maiden there who was engaged to a man named Joseph, a descendant of David. Her name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Gabriel came into her presence and greeted her, saying, “You have been shown great favor – the Lord is with you.”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Mary was much disturbed at his words, and was wondering to herself what such a greeting could mean,
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 when the angel spoke again, “Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And now, you will conceive and give birth to a son, and you will give him the name Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 The child will be great and will be called ‘Son of the Most High,’ and the Lord God will give him the throne of his ancestor David,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he will reign over the descendants of Jacob for ever; And to his kingdom there will be no end.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 “How can this be?” Mary asked the angel. “For I have no husband.”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 “The Holy Spirit will descend on you,” answered the angel, “and the Power of the Most High will overshadow you; and therefore the child will be called ‘holy,’ and ‘Son of God.’
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And Elizabeth, your cousin, is herself also expecting a son in her old age; and it is now the sixth month with her, though she is called barren;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 for no promise from God will fail to be fulfilled.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 “I am the servant of the Lord,” exclaimed Mary. “Let it be with me as you have said.” Then the angel left her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Soon after this Mary set out, and made her way quickly into the hill-country, to a town in Judah;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and there she went into Zechariah’s house and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 When Elizabeth heard Mary’s greeting, the child moved within her, and Elizabeth herself was filled with the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and cried aloud, “Blessed are you among women, and blessed is your unborn child!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 But how have I this honor, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, as soon as your greeting reached my ears, the child moved within me with delight!
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Happy indeed is she who believed that the promise which she received from the Lord would be fulfilled.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said: “My soul exalts the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit delights in God my Savior,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for he has looked with favor on his humble servant girl. From now on all generations will call me blessed!
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 “For the Almighty has done great things for me, and holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 He has mercy on those who revere him in every generation.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 “Mighty are the deeds of his arm! He has scattered the self-satisfied proud,
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 he has cast down the mighty from their thrones, and he uplifts the humble,
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 he has filled the hungry with good things, and the rich he has sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 “He has stretched out his hand to his servant Israel, ever mindful of his mercy,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 as he promised to our ancestors, to Abraham and his descendants for ever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned to her home.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 When Elizabeth’s time came, she gave birth to a son;
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 and her neighbors and relatives, hearing of the great goodness of the Lord to her, came to share her joy.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 A week later they met to circumcise the child, and were about to call him Zechariah after his father,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 when his mother spoke up, “No, he is to be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 “You have no relation of that name!” they exclaimed;
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 and they made signs to the child’s father, to find out what he wished the child to be called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Asking for a writing tablet, he wrote the words – ‘His name is John.’ Everyone was surprised
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 and immediately Zechariah recovered his voice and the use of his tongue, and began to bless God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 All their neighbors were awe-struck at this, and throughout the hill-country of Judea the whole story was much talked about.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 All who heard it kept it in mind, asking one another – “What can this child be destined to become?” For the Power of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Then his father Zechariah was filled with the Holy Spirit, and, speaking under inspiration, said:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blessed is the Lord, the God of Israel, who has visited his people and wrought their deliverance,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and has raised up for us the strength of our salvation in the house of his servant David –
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 as he promised by the lips of his holy prophets of old – (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies and from the hands of all who hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 showing mercy to our ancestors, and mindful of his sacred covenant.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 This was the oath which he swore to our ancestor Abraham –
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 that we should be rescued from the hands of our enemies,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 and should serve him without fear in holiness and righteousness, in his presence all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, will be called prophet of the Most High, for you will go before the Lord to make ready his way,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give his people the knowledge of salvation through the forgiveness of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the tender mercy of our God, whereby the dawn will break on us from heaven,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to give light to those who live in darkness and the shadow of death, and guide our feet into the way of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 The child grew and became strong in spirit, and he lived in the wilds until the time came for his appearance before Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >