< Matthew 26 >

1 When Jesus had finished teaching all of that, he said to his disciples,
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 ‘You know that in two days time the Festival of the Passover will be here; and that the Son of Man is to be given up to be crucified.’
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Then the chief priests and the elders of the people met in the house of the high priest, who was called Caiaphas,
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 and plotted together to arrest Jesus by stealth and put him to death;
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 but they said, ‘Not during the Festival, or the people may riot.’
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 After Jesus had reached Bethany, and while he was in the house of Simon the leper,
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 a woman came up to him with an alabaster jar of very costly perfume, and poured the perfume on his head as he sat at the table.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 The disciples were indignant at seeing this. ‘What is this waste for?’ they exclaimed.
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 ‘It could have been sold for a large sum, and the money given to poor people.’
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 ‘Why are you troubling the woman?’ Jesus said, when he noticed it. ‘For this is a beautiful deed that she has done to me.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 You always have the poor with you, but you will not always have me.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 In pouring this perfume on my body, she prepares me for my burial.
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 I tell you, wherever, in the whole world, this good news is proclaimed, what this woman has done will be told in memory of her.’
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 It was then that one of the Twelve, named Judas Iscariot, made his way to the chief priests,
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 and said ‘What are you willing to give me, if I betray Jesus to you?’ The Priests counted him out thirty pieces of silver as payment.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 So from that time Judas looked for an opportunity to betray Jesus.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 On the first day of the Festival of the unleavened bread, the disciples came up to Jesus, and said, ‘Where do you wish us to make preparations for you to eat the Passover?’
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 ‘Go into the city to a certain man,’ he answered, ‘and say to him “The teacher says – My time is near. I will keep the Passover with my disciples at your house.”’
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 The disciples did as Jesus directed them, and prepared the Passover.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 In the evening Jesus took his place with the twelve disciples,
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 and, while they were eating, he said, ‘I tell you that one of you will betray me.’
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 In great grief they began to say to him, one by one, ‘Can it be I, Master?’
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 ‘The one who dipped his bread beside me in the dish,’ replied Jesus, ‘is the one who will betray me.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 True, the Son of Man must go, as scripture says of him, yet alas for that man by whom the Son of Man is being betrayed! For that man it would be better never to have been born!’
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 Judas, who was betraying him, turned to him and said, ‘Can it be I, Rabbi?’ ‘It is,’ answered Jesus.
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 While they were eating, Jesus took some bread, and, after saying the blessing, broke it and, as he gave it to his disciples, said, ‘Take it and eat it; this is my body.’
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 Then he took a cup, and, after saying the thanksgiving, gave it to them, with the words, ‘Drink from it, all of you;
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 for this is my covenant blood, which is poured out for many for the forgiveness of sins.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 I tell you that I will never, after this, drink of this juice of the grape, until that day when I will drink it new with you in the kingdom of my Father.’
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 They then sang a hymn, and went out to the Mount of Olives.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Then Jesus said to them, ‘Even you will all fall away from me tonight. Scripture says – “I will strike down the shepherd, and the sheep of the flock will be scattered.”
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 But, after I have risen, I will go before you into Galilee.’
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 ‘If everyone else falls away from you,’ Peter answered, ‘I will never fall away!’
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 ‘I tell you,’ replied Jesus, ‘that this very night, before the cock crows, you will disown me three times!’
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 ‘Even if I must die with you,’ Peter exclaimed, ‘I will never disown you!’ All the disciples spoke in the same way.
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Then Jesus came with them to a garden called Gethsemane, and he said to his disciples, ‘Sit down here while I go and pray over there.’
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 Taking with him Peter and the two sons of Zebedee, he began to show signs of sadness and deep distress of mind.
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 ‘I am sad at heart,’ he said, ‘sad even to death; wait here and watch with me.’
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 Going on a little further, he threw himself on his face in prayer. ‘My Father,’ he said, ‘if it is possible, let me be spared this cup; only, not as I will, but as you will.’
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 Then he came to his disciples, and found them asleep. ‘What!’ he said to Peter, ‘could none of you watch with me for one hour?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 Watch and pray so that you don’t fall into temptation. True, the spirit is eager, but human nature is weak.’
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Again, a second time, he went away, and prayed. ‘My Father,’ he said, ‘if I cannot be spared this cup, but must drink it, your will be done!’
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 And coming back again he found them asleep, for their eyes were heavy.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 So he left them, and went away again, and prayed a third time, again saying the same words.
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Then he came to the disciples, and said, ‘Sleep on now, and rest yourselves. Look – my time is close at hand, and the Son of Man is being betrayed into the hands of wicked people.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 Up, and let us be going. Look! My betrayer is close at hand.’
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 And, while he was still speaking, Judas, who was one of the Twelve, came in sight; and with him was a great crowd of people, with swords and clubs, sent from the chief priests and elders of the people.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 Now the betrayer had arranged a signal with them. ‘The man whom I kiss,’ he had said, ‘will be the one; arrest him.’
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 So he went up to Jesus at once, and exclaimed, ‘Welcome, Rabbi!’ and kissed him;
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 at which Jesus said to him, ‘Friend, do what you have come for.’ The men went up, seized Jesus, and arrested him.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 Suddenly one of those who were with Jesus stretched out his hand, and drew his sword, and striking the high priest’s servant, cut off his ear.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 ‘Sheathe your sword,’ Jesus said, ‘for all who draw the sword will be put to the sword.
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Do you think that I cannot ask my Father for help, when he would at once send to my aid more than twelve legions of angels?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 But in that case how would the scriptures be fulfilled, which say that this must be?’
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 Jesus at the same time said to the crowds, ‘Have you come out, as if after a robber, with swords and clubs, to take me? I have sat teaching day after day in the Temple Courts, and yet you did not arrest me.’
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 The whole of this occurred in fulfilment of the prophetic scriptures. Then the disciples all forsook him and fled.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 Those who had arrested Jesus took him to Caiaphas, the high priest, where the teachers of the Law and elders had assembled.
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 Peter followed him at a distance as far as the high priest’s courtyard, to see the outcome.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 Meanwhile the chief priests and the whole of the High Council were trying to get such false evidence against Jesus, as would warrant putting him to death,
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 but they did not find any, although many came forward with false evidence. Later on, however, two men came forward and said,
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 ‘This man said “I am able to destroy the Temple of God, and to build it in three days.”’
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 Then the high priest stood up, and said to Jesus, ‘Have you no answer? What is this evidence which these men are giving against you?’
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 But Jesus remained silent. The high priest said to him, ‘I order you, by the living God, to tell us whether you are the Christ, the Son of God.’
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 ‘It is true,’ Jesus answered, ‘Moreover I tell you all that hereafter you will see the Son of Man sitting on the right hand of the Almighty, and coming on the clouds of the heavens.’
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Then the high priest tore his robes. ‘This is blasphemy!’ he exclaimed. ‘Why do we want any more witnesses? You have just heard his blasphemy!
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 What is your decision?’ They answered, ‘He deserves death.’
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Then they spat in his face, and struck him, while others dealt blows at him, saying as they did so,
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 ‘Now play the prophet for us, you Christ! Who was it that struck you?’
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 Peter, meanwhile, was sitting outside in the courtyard; and a maidservant came up to him, and exclaimed, ‘Why, you were with Jesus the Galilean!’
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 But Peter denied it before them all. ‘I do not know what you mean,’ he replied.
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 When he had gone out into the gateway, another maid saw him, and said to those who were there, ‘This man was with Jesus of Nazareth!’
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 Again he denied it with an oath, ‘I do not know the man!’
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 But soon afterwards those who were standing by came up and said to Peter, ‘You also are certainly one of them; why, even your way of speaking proves it!’
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Then Peter said, ‘I swear that I do not know the man! May God punish me if I am lying!’ At that moment a cock crowed;
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 and Peter remembered the words which Jesus had said – “Before a cock has crowed, you will disown me three times”; and he went outside, and wept bitterly.
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.

< Matthew 26 >