< Matthew 16 >

1 Here the Pharisees and Sadducees came up, and, to test Jesus, requested him to show them some sign from the heavens.
Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama.
2 But Jesus answered, ‘In the evening you say “It will be fine weather, for the sky is as red as fire.”
Amma ya amsa ya ce masu, “Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'
3 But in the morning you say “Today it will be stormy, for the sky is as red as fire and threatening.” You learn to read the sky; yet you are unable to read the signs of the times!
Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba.
4 A wicked and unfaithful generation is asking for a sign, but no sign will be given it except the sign of Jonah.’ So he left them and went away.
Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa.” Daga nan sai Yesu ya tafi.
5 Now the disciples had crossed to the opposite shore, and had forgotten to take any bread.
Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa,
6 Presently Jesus said to them, ‘Take care and be on your guard against the leaven of the Pharisees and Sadducees.’
Yesu ya ce masu, “Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa.”
7 But the disciples began talking among themselves about their having brought no bread.
Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, “Ko saboda bamu kawo gurasa bane.”
8 On noticing this, Jesus said, ‘Why are you talking among yourselves about your being short of bread, you of little faith?
Yesu yana sane da wannan sai ya ce, “Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
9 Don’t you yet see, nor remember the five loaves for the five thousand, and how many baskets you took away?
Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba?
10 Nor yet the seven loaves for the four thousand, and how many basketfuls you took away?
Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
11 How is it that you do not see that I was not speaking about bread? Be on your guard against the leaven of the Pharisees and Sadducees.’
Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa.”
12 Then they understood that he had told them to be on their guard, not against the leaven of bread, but against the teaching of the Pharisees and Sadducees.
Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
13 On coming into the region of Caesarea Philippi, Jesus asked his disciples this question – ‘Who do people say that the Son of Man is?’
A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, “Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake?
14 ‘Some say John the Baptist,’ they answered, ‘Others, however, say that he is Elijah, while others again say Jeremiah, or one of the prophets.’
Suka ce, “Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa.”
15 ‘But you,’ he said, ‘who do you say that I am?’
Ya ce masu, “Amma ku wa kuke ce da ni?”
16 To this Simon Peter answered, ‘You are the Christ, the Son of the living God.’
Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai.”
17 ‘Blessed are you, Simon, Son of Jonah,’ Jesus replied. ‘For no human being has revealed this to you, but my Father who is in heaven.
Yesu ya amsa ya ce masa, “Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama.
18 Yes, and I say to you, your name is “Peter” – a Rock, and on this rock I will build my church, and the gates of Hades will not prevail over it. (Hadēs g86)
Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba. (Hadēs g86)
19 I will give you the keys of the kingdom of heaven. Whatever you forbid on earth will be held in heaven to be forbidden, and whatever you allow on earth will be held in heaven to be allowed.’
Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama,”
20 Then he charged his disciples not to tell anyone that he was the Christ.
Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
21 At that time Jesus Christ began to explain to his disciples that he must go to Jerusalem, and undergo much suffering at the hands of the elders, and chief priests, and teachers of the Law, and be put to death, and rise on the third day.
Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku.
22 But Peter took Jesus aside, and began to rebuke him. ‘Master,’ he said, ‘please God that will never be your fate!’
Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, “Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba.”
23 Jesus, however, turning to Peter, said, ‘Out of my way, Satan! You are a hindrance to me; for you look at things, not as God does, but as person does.’
Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane.”
24 Then Jesus said to his disciples, ‘If anyone wishes to walk in my steps, they must renounce self, and take up their cross, and follow me.
Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni.
25 For whoever wishes to save his life will lose it, and whoever, for my sake, loses his life will find it.
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi.
26 What good will it do a person to gain the whole world, if he forfeits his life? Or what will a person give that is of equal value with his life?
Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
27 For the Son of Man is to come in his Father’s glory, with his angels, and then he will give to everyone what his actions deserve.
Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa.
28 I tell you, some of those who are standing here will not know death until they have seen the Son of Man coming into his kingdom.’
Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa.”

< Matthew 16 >