< Matthew 16 >

1 Here the Pharisees and Sadducees came up, and, to test Jesus, requested him to show them some sign from the heavens.
Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
2 But Jesus answered, ‘In the evening you say “It will be fine weather, for the sky is as red as fire.”
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
3 But in the morning you say “Today it will be stormy, for the sky is as red as fire and threatening.” You learn to read the sky; yet you are unable to read the signs of the times!
da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
4 A wicked and unfaithful generation is asking for a sign, but no sign will be given it except the sign of Jonah.’ So he left them and went away.
Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
5 Now the disciples had crossed to the opposite shore, and had forgotten to take any bread.
Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
6 Presently Jesus said to them, ‘Take care and be on your guard against the leaven of the Pharisees and Sadducees.’
Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
7 But the disciples began talking among themselves about their having brought no bread.
Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
8 On noticing this, Jesus said, ‘Why are you talking among yourselves about your being short of bread, you of little faith?
Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
9 Don’t you yet see, nor remember the five loaves for the five thousand, and how many baskets you took away?
Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
10 Nor yet the seven loaves for the four thousand, and how many basketfuls you took away?
Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
11 How is it that you do not see that I was not speaking about bread? Be on your guard against the leaven of the Pharisees and Sadducees.’
Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
12 Then they understood that he had told them to be on their guard, not against the leaven of bread, but against the teaching of the Pharisees and Sadducees.
Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
13 On coming into the region of Caesarea Philippi, Jesus asked his disciples this question – ‘Who do people say that the Son of Man is?’
Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
14 ‘Some say John the Baptist,’ they answered, ‘Others, however, say that he is Elijah, while others again say Jeremiah, or one of the prophets.’
Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
15 ‘But you,’ he said, ‘who do you say that I am?’
Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
16 To this Simon Peter answered, ‘You are the Christ, the Son of the living God.’
Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
17 ‘Blessed are you, Simon, Son of Jonah,’ Jesus replied. ‘For no human being has revealed this to you, but my Father who is in heaven.
Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
18 Yes, and I say to you, your name is “Peter” – a Rock, and on this rock I will build my church, and the gates of Hades will not prevail over it. (Hadēs g86)
Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs g86)
19 I will give you the keys of the kingdom of heaven. Whatever you forbid on earth will be held in heaven to be forbidden, and whatever you allow on earth will be held in heaven to be allowed.’
Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
20 Then he charged his disciples not to tell anyone that he was the Christ.
Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
21 At that time Jesus Christ began to explain to his disciples that he must go to Jerusalem, and undergo much suffering at the hands of the elders, and chief priests, and teachers of the Law, and be put to death, and rise on the third day.
Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
22 But Peter took Jesus aside, and began to rebuke him. ‘Master,’ he said, ‘please God that will never be your fate!’
Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
23 Jesus, however, turning to Peter, said, ‘Out of my way, Satan! You are a hindrance to me; for you look at things, not as God does, but as person does.’
Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
24 Then Jesus said to his disciples, ‘If anyone wishes to walk in my steps, they must renounce self, and take up their cross, and follow me.
Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
25 For whoever wishes to save his life will lose it, and whoever, for my sake, loses his life will find it.
Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
26 What good will it do a person to gain the whole world, if he forfeits his life? Or what will a person give that is of equal value with his life?
Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
27 For the Son of Man is to come in his Father’s glory, with his angels, and then he will give to everyone what his actions deserve.
Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
28 I tell you, some of those who are standing here will not know death until they have seen the Son of Man coming into his kingdom.’
“Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”

< Matthew 16 >