< 2 Corinthians 2 >

1 For my own sake, as well, I decided not to pay you another painful visit.
Saboda haka na yanke shawara ba zan sāke kawo muku ziyara ta ɓacin rai ba.
2 If it is I who cause you pain, why, who is there to cheer me, except the person whom I am paining?
Gama in na sa ku baƙin ciki, wa ya rage yă faranta mini zuciya, in ba ku waɗanda na sa baƙin cikin ba?
3 So I wrote as I did because I was afraid that if I had come, I should have been pained by those who ought to have made me glad; for I felt sure that it was true of you all that my joy was in every case yours also.
Na rubuta yadda na yi ne saboda sa’ad da na iso kada waɗanda ya kamata su faranta mini rai, su sa ni baƙin ciki. Na amince da ku duka a kan farin cikina naku ne ku duka.
4 I wrote to you in sore trouble and distress of heart and with many tears, not to give you pain, but to let you see how intense a love I have for you.
Gama na rubuta muku ne cikin baƙin ciki mai yawa da ɓacin zuciya har ma da hawaye mai yawa, ba don in sa ku baƙin ciki ba ne, a’a, sai dai domin in nuna muku zurfin ƙaunar da nake yi muku.
5 Now whoever has caused the pain has not so much pained me, as he has, to some extent – not to be too severe – pained every one of you.
In wani ya jawo baƙin ciki, ba ni kaɗai ya jawo wa ba, amma a wani fanni, sai in ce dukanku ne ya jawo wa, ba na faɗa haka don in matsa muku lamba ba ne.
6 The man to whom I refer has been sufficiently punished by the penalty inflicted by the majority of you;
Irin wannan mutum, horon da yawancin mutane suka yi masa ya isa haka.
7 so that now you must take the opposite course, and forgive and encourage him, or else he may be overwhelmed by the intensity of his pain.
Yanzu fa, a maimako, gara ku yafe masa, ku kuma ta’azantar da shi, don kada baƙin ciki mai yawa yă sha kansa.
8 So I entreat you to assure him of your love.
Saboda haka, ina roƙonku, ku sāke nuna masa ƙaunarku.
9 I had this further object, also, in what I wrote – to find out whether you might be relied on to be obedient in everything.
Abin da ya sa na rubuta muku shi ne don in ga ko za ku jimre da gwajin nan, kuna kuma yin biyayya ta kowace hanya.
10 Anyone you forgive, I forgive them, too. Indeed, for my part, whatever I have forgiven (if I have had to forgive anything), I have forgiven for your sakes, in the presence of Christ,
In kuka gafarta wa wani, ni ma na gafarta masa. Abin da na gafarta kuwa, in har ma da abin gafartawa, saboda ku ne na gafarta masa, albarkacin Kiristi,
11 so as to prevent Satan from taking advantage of us; for we are not ignorant of his devices.
don kada Shaiɗan yă rinjaye mu. Da yake muna sane da dabarunsa.
12 When I went to the district round Troas to tell the good news of the Christ, even though there was an opening for serving the Master,
To, sa’ad da na tafi Toruwas don in yi wa’azin bisharar Kiristi, ko da yake na tarar cewa Ubangiji ya buɗe mini ƙofa,
13 I could get no peace of mind because I failed to find Titus, my friend; so I took leave of the people there, and went on to Macedonia.
duk da haka, ban sami salama a zuciyata ba domin ban sami ɗan’uwana Titus a can ba. Sai na yi bankwana da su na wuce zuwa Makidoniya.
14 All thanks to God, who, through our union with the Christ, leads us in one continual triumph, and uses us to spread the sweet perfume of the knowledge of him in every place.
Amma godiya ga Allah, wanda kullum yake bi da mu da nasara cikin Kiristi, kuma ta wurinmu, yana baza ƙanshin nan na sanin Kiristi a ko’ina.
15 For we are the fragrance of Christ ascending to God – both among those who are in the path of salvation and among those who are in the path to ruin.
Don kuwa, a wurin Allah mu ƙanshin Kiristi ne cikin waɗanda ake ceto, da kuma waɗanda suke hanyar hallaka.
16 To the latter we are a stench which arises from death and tells of death; to the former a fragrance which arises from life and tells of life. But who is equal to such a task?
Ga wani, mu warin mutuwa ne, amma ga wani kuwa, mu ƙanshin rai ne. Wa ya isa yă yi irin wannan aikin?
17 Unlike many people, we are not in the habit of making profit out of God’s message; but in all sincerity, and bearing God’s commission, we speak before him in union with Christ.
Ba ma tallar maganar Allah don riba yadda waɗansu mutane da yawa suke yi. A maimakon haka, muna magana cikin Kiristi a gaban Allah da gaskiya, kamar mutanen da aka aika daga Allah.

< 2 Corinthians 2 >