< 1 John 2 >

1 My children, I am writing to you to keep you from sinning. But if anyone does sin, we have an advocate with the Father – Jesus Christ, the righteous.
’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
2 He is the atoning sacrifice for our sins, and not for ours only, but the sins of the whole world.
Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
3 It is by keeping God’s commands that we can be sure we know him.
Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
4 Whoever says ‘I know him,’ but does not keep his commands, is a liar. The truth has no place in them.
Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
5 But the person who keeps God’s word, in them the love of God has indeed reached its perfection. This is how we can be sure we are in him:
Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
6 whoever claims to live in him should live just as Jesus did.
Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
7 Dear friends, it is no new command that I am writing to you, but an old command, which you have had from the beginning. That old command is the message you have already heard.
Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
8 Yet, in a way, it is a new command that I am writing to you – which is shown true in Christ’s life and in yours – for the darkness is passing away and the true light is already shining.
Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
9 The person who says that they are in the light, and yet hates others, is still in the darkness.
Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
10 The person who loves others is always in the light, and there is nothing within them to cause them to stumble.
Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
11 The person who hates is in the dark. They stumble along in the darkness; they do not know where they are going because the darkness blinds them.
Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
12 Little children, I am writing to you because your sins have been forgiven for Christ’s sake.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
13 Parents, I am writing to you because you have come to know him who has been from the beginning. Young people, I am writing to you because you have conquered the evil one. Children, I write to you because you have come to know the Father.
Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
14 Parents, I write to you because you have learned to know him who has been from the beginning. Young people, I write to you because you are strong, and God’s message is always in your hearts, and you have conquered the evil one.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
15 Do not love the world or what the world can offer. When anyone loves the world, there is no love for the Father in them.
Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
16 For all that the world can offer – the desires for physical pleasure, the enticements to the eye, the arrogance of wealth – belongs, not to the Father, but to the world.
Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
17 And the world, and all that it gratifies, is passing away, but they who do God’s will remain for ever. (aiōn g165)
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn g165)
18 My children, it is the last hour. You were told that an antichrist was coming; and many antichrists have already arisen. This is why we know that this is the last hour.
’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
19 These people come from our ranks, but they were never truly part of us – if they had been then they would have stayed with us. They left so it would be clear that none of them really belonged to us.
Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
20 You, however, have been annointed by the Holy One. You all know the truth.
Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
21 I am not writing to you because you do not know the truth, but because you do know it, and because no lie can come from the truth.
Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
22 Who is a liar, if not the one who denies that Jesus is the Christ? That person is the antichrist – one who rejects the Father and the Son.
Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
23 No one who rejects the Son has the Father; to acknowledge the Son is to have the Father also.
Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
24 As for you, you must let what you have heard from the beginning continue to live in you. If what you heard from the beginning dwells in you, you will remain both in the Son and the Father.
Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
25 And this is what he himself promised us – eternal life! (aiōnios g166)
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios g166)
26 In writing this to you, I have in mind those who are trying to mislead you.
Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
27 As for you, the anointing which you received from him remains with you. You do not need anyone to teach you. His anointing teaches you about everything. What it teaches you is true, it is not a lie. Do what it has taught you: abide in him.
Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
28 Yes, my children, remain in him, so that when he appears our confidence doesn’t fail us, and we are not ashamed to meet him at his coming.
Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
29 Since you know he is righteous, you realise that everyone who does what is right is his child.
In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.

< 1 John 2 >