< Luke 5 >

1 Now while the multitude pressed on him and heard ha D'var Elohim · the Word of God·, he was standing by the lake of Gennesaret.
Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
2 He saw two boats standing by the lake, but the fishermen had gone out of them, and were washing their nets.
Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
3 He entered into one of the boats, which was Simeon [Hearing]’s, and asked him to put out a little from the land. He sat down and taught the multitudes from the boat.
Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
4 When he had finished speaking, he said to Simeon [Hearing], “Put out into the deep, and let down your nets for a catch.”
Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
5 Simeon [Hearing] answered him, “Master, we worked all night, and took nothing; but at your word I will let down the net.”
Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
6 When they had done this, they caught a great multitude of fish, and their net was breaking.
Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
7 They beckoned to their partners in the other boat, that they should come and help them. They came, and filled both boats, so that they began to sink.
Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8 But Simeon Peter [Hearing Rock], when he saw it, fell down at Yeshua [Salvation]'s knees, saying, “Depart from me, for I am a sinful man, Lord.”
Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
9 For he was amazed, and all who were with him, at the catch of fish which they had caught;
Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
10 and so also were James [Surplanter] and John [Yah is gracious], sons of Zebedee [Bestowed by Yah], who were partners with Simeon [Hearing]. Yeshua [Salvation] said to Simeon [Hearing], “Don’t be afraid. From now on you will be catching people alive.”
Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
11 When they had brought their boats to land, they left everything, and followed him.
Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12 While he was in one of the cities, behold, there was a man full of tzara'at ·leprosy·. When he saw Yeshua [Salvation], he fell on his face, and begged him, saying, “Lord, if you want to, you can make me clean.”
Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
13 He stretched out his hand, and touched him, saying, “I want to. Be made clean.” Immediately the tzara'at ·leprosy· left him.
Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14 He commanded him to tell no one. “Instead, as a testimony to the people, go straight to the priest and make an offer for your cleansing, as Moses [Drawn out] commanded.”
Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
15 But the report concerning him spread much more, and great multitudes came together to hear, and to be healed by him of their infirmities.
Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
16 But he withdrew himself into the desert, and prayed.
Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17 On one of those days, he was teaching; and there were Pharisees [Separated] and Torah-Teachers sitting by, who had come out of every village of Galilee [District, Circuit], Judea [Praise], and Jerusalem [City of peace]. The power of MarYah [Master Yahweh] was with him to heal them.
Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18 Behold, men brought a paralyzed man on a cot, and they sought to bring him in to lay before Yeshua [Salvation].
A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Not finding a way to bring him in because of the multitude, they went up to the housetop, and let him down through the tiles with his cot into the middle before Yeshua [Salvation].
Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20 Seeing their trusting faith, he said to him, “Man, your sins are forgiven you.”
Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
21 The Torah-Teachers and the Pharisees [Separated] began to reason, saying, “Who is this that speaks blasphemies? Who can forgive sins, but God alone?”
Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
22 But Yeshua [Salvation], perceiving their thoughts, answered them, “Why are you reasoning so in your hearts?
Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
23 Which is easier to say, ‘Your sins are forgiven you;’ or to say, ‘Arise and walk?’
Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
24 But that you may know that the Son of Man has authority on earth to forgive sins” (he said to the paralyzed man), “I tell you, arise, and take up your cot, and go to your house.”
Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
25 Immediately he rose up before them, and took up that which he was laying on, and departed to his house, glorifying God.
Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
26 Amazement took hold on all, and they glorified God. They were filled with fear, saying, “We have seen strange things today.”
Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
27 After these things he went out, and saw a tax collector named Levi [United with] sitting at the tax office, and said to him, “Follow me!”
Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
28 He left everything, and rose up and followed him.
Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29 Levi [United with] made a great feast for him in his house. There was a great crowd of tax collectors and others who were reclining with them.
Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
30 Their Torah-Teachers and the Pharisees [Separated] murmured against his disciples, saying, “Why do you eat and drink with the tax collectors and sinners?”
Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
31 Yeshua [Salvation] answered them, “Those who are healthy have no need for a physician, but those who are sick do.
Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
32 I have not come to call the upright, but sinners to teshuvah ·complete repentance·.”
Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 They said to him, “Why do John [Yah is gracious]’s disciples often fast and pray, likewise also the disciples of the Pharisees [Separated], but yours eat and drink?”
Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
34 He said to them, “Can you make the friends of the bridegroom fast, while the bridegroom is with them?
Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
35 But the days will come when the bridegroom will be taken away from them. Then they will fast in those days.”
Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
36 He also told a parable to them. “No one puts a piece from a new garment on an old garment, or else he will tear the new, and also the piece from the new will not match the old.
Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37 No one puts new wine into old wine skins, or else the new wine will burst the skins, and it will be spilled, and the skins will be destroyed.
Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
38 But new wine must be put into fresh wine skins, and both are preserved.
Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
39 No man having drunk old wine immediately desires new, for he says, ‘The old is better.’”
Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”

< Luke 5 >