< Luke 22 >

1 Now the feast of unleavened bread, which is called the passover, was drawing near;
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 and the chief priests and the scribes were seeking how they might kill him; for they feared the people.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 And Satan entered into Judas called Iscariot, who was of the number of the twelve.
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 And he went away, and consulted with the chief priests and captains, how he might deliver him up to them.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 And they were glad, and covenanted to give him money.
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 And he agreed with them, and sought a good opportunity to deliver him up to them in the absence of the multitude.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Then came the day of unleavened bread, when the passover must be killed;
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 and he sent Peter and John, saying, Go and make ready for us the passover, that we may eat it.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 And they said to him, Where wilt thou that we make it ready?
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 And he said to them, Lo! when ye have entered the city, there will meet you a man bearing a pitcher of water; follow him into the house where he goeth in;
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 and ye shall say to the master of the house, The Teacher saith to thee, Where is the guest-chamber, where I may eat the passover with my disciples?
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 And he will show you a large upper room furnished; there make ready.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 And they went and found as he had said to them; and they made ready the passover.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 And when the hour had come, he placed himself at table, and the apostles with him.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 And he said to them, Earnestly have I desired to eat this passover with you, before I suffer.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 For I say to you, that I shall eat it no more, until it be fulfilled in the kingdom of God.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 And he took a cup, and gave thanks, and said, Take this, and divide it among yourselves.
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 For I say to you, that I shall not drink henceforth of the fruit of the vine, until the kingdom of God shall have come.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 And he took a loaf, and gave thanks, and broke it, and gave it to them, saying, This is my body, which is given for you; this do in remembrance of me.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 And in like manner he took the cup after supper, saying, This cup is the new covenant in my blood, which is about to be shed for you.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 But lo! the hand of him that betrayeth me is with me on the table.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 For the Son of man indeed goeth away, as it hath been determined; but woe to that man by whom he is betrayed.
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 And they began to inquire among themselves, which of them it was that was about to do this.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 And there arose also a contention among them, which of them should be accounted the greatest.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 And he said to them, The kings of the nations rule as lords over them, and they who exercise authority over them are called benefactors.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 But it is not to be so with you; but let the greatest among you be as the youngest; and he that is chief, as he that serveth.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 For which is greater? he who reclineth at the table, or he who serveth? Is not he that reclineth at the table? But I am in the midst of you as he who serveth.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 Ye however are they who have continued steadfastly with me in my trials.
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 And I appoint to you a kingdom, as my Father appointed to me;
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 that ye may eat and drink at my table in my kingdom; and ye shall sit on thrones, judging the twelve tribes of Israel.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 Simon, Simon, lo! Satan hath asked for you, that he may sift you as wheat.
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 But I have prayed for thee, that thy faith fail not. And do thou, when thou hast returned to me, strengthen thy brethren.
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 And he said to him, Lord, I am ready to go with thee both to prison and to death.
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 And he said, I tell thee, Peter, a cock will not crow this day, till thou hast thrice denied that thou knowest me.
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 And he said to them, When I sent you without purse, or bag, or sandals, were ye in need of anything? And they said, Of nothing. Then he said to them,
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 But now, he that hath a purse, let him take it, and likewise a bag; and he that hath not, let him sell his garment, and buy a sword.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 For I say to you, that this which is written must be accomplished in me: “And he was reckoned among transgressors.” For that which concerneth me also hath an end.
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 And they said, Lord, behold, here are two swords. And he said to him, It is enough!
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 And going out, he went, as he was wont, to the Mount of Olives; and the disciples followed him.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 And when he was at the place, he said to them, Pray that ye may not enter into temptation.
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 And he withdrew from them about a stone's throw; and kneeling down he prayed,
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 saying, Father, if thou art willing to remove this cup from me—yet not my will, but thine be done!
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 And there appeared to him an angel from heaven, strengthening him.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 And being in an agony, he prayed more earnestly. And his sweat was as it were great drops of blood falling to the ground.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 And rising up from prayer, he came to the disciples, and found them sleeping for sorrow,
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 and said to them, Why sleep ye? Rise, and pray that ye may not enter into temptation.
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 While he was yet speaking, lo! a multitude, and he that was called Judas, one of the twelve, was at the head of them; and he drew near to Jesus to kiss him.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 But Jesus said to him, Judas, dost thou betray the Son of man with a kiss?
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 And they who were about him, seeing what would follow, said, Lord, shall we smite with the sword?
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 And one of them smote the servant of the high-priest, and cut off his right ear.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 But Jesus answering said, Permit thus far; and touched his ear, and healed him.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Then Jesus said to the chief priests and captains of the temple and elders who had come to him, Ye have come out as against a robber, with swords and clubs;
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 when I was daily with you in the temple, ye did not put forth your hands against me; but this is your hour, and the power of darkness.
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 And they seized him, and led him away, and brought him into the house of the high-priest. And Peter followed afar off.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 And when they had kindled a fire in the midst of the court, and had sat down together, Peter sat down among them.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 But a certain maid-servant saw him sitting at the fire, and steadily looking at him said, This man also was with him.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 And he denied him, saying, Woman, I do not know him.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 And after a little while another saw him, and said, Thou also art one of them. And Peter said, Man, I am not.
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 And in about one hour's time, another confidently affirmed, saying, In truth this man also was with him; for he is a Galilaean.
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 And Peter said, Man, I know not what thou sayest. And immediately, while he was yet speaking, a cock crew.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 And the Lord turned and looked upon Peter; and Peter remembered the word of the Lord, that he had said to him, Before a cock crows this day, thou wilt thrice deny me.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 And he went out, and wept bitterly.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 And the men that held Jesus mocked him, and beat him;
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 and having blindfolded him, they asked him, saying, Prophesy, who is it that struck thee?
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 And many other things did they scoffingly say against him.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 And when it was day, the elders of the people, both chief priests and scribes, came together, and brought him before their council, saying,
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 If thou art the Christ, tell us. And he said to them, If I tell you, ye will not believe;
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 and if I ask, ye will not answer.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 But from this time the Son of man will sit on the right hand of the power of God.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 Then they all said, Art thou then the Son of God? And he said to them, Ye say what is true; for I am.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 And they said, What further need have we of testimony? For we have ourselves heard from his own mouth.
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”

< Luke 22 >