< Luke 1 >

1 Inasmuch as many have undertaken to arrange a narrative of those things which are fully believed among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 even as they were delivered to us by those who were eye-witnesses from the beginning and became ministers of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good to me also, having accurately traced up all things from the first, to write to thee a connected account, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that thou mightst know the exact truth with regard to those things in which thou wast instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, king of Judaea, a certain priest named Zachariah, of the course of Abijah; and he had a wife of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both righteous in the sight of God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both far advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, that, while he was serving as priest before God in the order of his course,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood the lot fell to him to go into the temple of the Lord and burn the incense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And the whole multitude of the people was praying without at the time of the incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him an angel of the Lord, standing on the right of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zachariah was troubled at the sight, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, Fear not, Zachariah; for thy prayer was heard, and thy wife Elizabeth shall bear thee a son; and thou shalt call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And thou wilt have joy and gladness, and many will rejoice for his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord; and will drink neither wine nor strong drink; and he will be filled with the Holy Spirit from his very birth.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the sons of Israel will he turn to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go before his face in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of fathers to children, and the disobedient to the wisdom of the righteous, to make ready for the Lord a prepared people.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zachariah said to the angel, Whereby shall I know this? for I am an old man, and my wife is far advanced in years.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answering said to him, I am Gabriel, who stand in the presence of God; and I was sent to speak to thee, and to tell thee these glad tidings.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And lo! thou shalt be silent, and not able to speak, until the day when these things shall come to pass, because thou didst not believe my words, which will be fulfilled in their season.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were looking for Zachariah, and wondering that he remained so long in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And on coming out, he was not able to speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the temple; and he was beckoning to them, and remained speechless.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his ministration were completed, that he returned to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after those days his wife Elizabeth conceived, and hid herself five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus hath the Lord dealt with me in the days wherein he looked on me to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in her sixth month the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee, called Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the virgin's name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel came in to her and said, Hail, thou that art highly favored! the Lord is with thee.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And she was troubled at the words, and was considering what this salutation could mean.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said to her, Fear not, Mary; for thou hast found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And lo! thou shalt conceive in thy womb, and hear a son, and shalt call his name Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Most High; and the Lord God will give to him the throne of David his father;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he shall reign over the house of Jacob for ever; and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then said Mary to the angel, How shall this be, since I know not a man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel answering said to her, The Holy Spirit will come upon thee, and the power of the Most High will overshadow thee; wherefore the holy one that is to be born will be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And lo! Elizabeth, thy kinswoman, she also hath conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who is called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For nothing will be impossible with God.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said, Lo, the handmaid of the Lord! May it be to me according to thy word. And the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary arose and went in those days into the hill-country with haste, into a city of Judah.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And she entered the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elizabeth heard the salutation of Mary, that the babe leaped in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and cried out with a loud voice, and said, Blessed art thou among women; and blessed is the fruit of thy womb!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And whence is this to me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For lo! as soon as the voice of thy salutation came to my ears, the babe leaped in my womb in exultation.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she who hath believed that there will be an accomplishment of those things which were told her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, My soul magnifieth the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit hath exulted in God my Saviour;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for he hath looked upon the low estate of his handmaiden. For lo! from this time all generations will call me blessed;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 for the Mighty One hath done great things for me; and holy is his name;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 and his mercy is from generation to generation on them that fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath wrought mightily with his arm; he hath scattered the proud in the device of their heart.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath cast down princes from thrones, and exalted men of low degree.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 The hungry he hath filled with good things, and the rich he hath sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath given help to Israel his servant, in remembrance of his mercy
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 toward Abraham and his offspring for ever, as he spoke to our fathers. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary abode with her about three months, and returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now Elizabeth's full time came that she should be delivered; and she brought forth a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbors and her kinsfolk heard that the Lord had showed great mercy toward her; and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass that on the eighth day they came to circumcise the child; and they were about to call him Zachariah, after the name of his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother answering said, Not so; but he shall be called John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, There is no one of thy kindred that is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, how he would have him named.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he asked for a writing-tablet, and wrote, saying, His name is John. And they all marveled.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue was loosed; and he spoke, blessing God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came on all that dwelt around them; and all these things were talked of throughout the whole of the hill-country of Judaea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all that heard them laid them up in their hearts, saying, What then will this child be? For the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zachariah his father was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord, the God of Israel! for he hath visited and redeemed his people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and hath raised up a horn of salvation for us in the house of David his servant, —
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 as he spoke by the mouth of his holy prophets of old, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all that hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to accomplish his mercy toward our fathers, and to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he swore to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 to grant to us, that being delivered from the hand of our enemies, we might worship him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and righteousness before him, all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, shalt be called a prophet of the Most High; for thou shalt go in advance before the face of the Lord to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give knowledge of salvation to his people in the remission of their sins
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the tender mercy of our God, whereby the day-spring from on high hath visited us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to give light to those sitting in darkness and the shadow of death, to guide our feet into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and waxed strong in spirit; and was in the deserts till the day of his manifestation to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >