< John 11 >

1 Now a certain man was sick, Lazarus from Bethany, of the village of Mary and her sister, Martha.
To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
2 It was that Mary who had anointed the Lord with ointment, and wiped his feet with her hair, whose brother, Lazarus, was sick.
Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
3 The sisters therefore sent to him, saying, "Lord, look, the one you love is sick."
Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
4 But when Jesus heard it, he said, "This sickness is not to death, but for the glory of God, that God's Son may be glorified by it."
Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
5 Now Jesus loved Martha, and her sister, and Lazarus.
Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
6 When therefore he heard that he was sick, he stayed two days in the place where he was.
Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
7 Then after this he said to the disciples, "Let us go into Judea again."
Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
8 The disciples told him, "Rabbi, the Jewish leaders were just trying to stone you, and are you going there again?"
Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
9 Jesus answered, "Are there not twelve hours of daylight? If anyone walks in the day, he does not stumble, because he sees the light of this world.
Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
10 But if anyone walks in the night, he stumbles, because the light is not in him."
Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
11 He said these things, and after that, he said to them, "Our friend, Lazarus, has fallen asleep, but I am going so that I may awake him out of sleep."
Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
12 Then the disciples said to him, "Lord, if he has fallen asleep, he will recover."
Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
13 Now Jesus had spoken of his death, but they thought that he spoke of taking rest in sleep.
Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
14 So Jesus said to them plainly then, "Lazarus is dead.
Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
15 I am glad for your sakes that I was not there, so that you may believe. Nevertheless, let us go to him."
amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
16 Thomas therefore, who is called Didymus, said to his fellow disciples, "Let us go also, that we may die with him."
Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
17 So when Jesus came, he found that he had been in the tomb four days already.
Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
18 Now Bethany was near Jerusalem, about two miles away.
Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
19 Many of the Jewish people had come to Martha and Mary, to console them concerning their brother.
Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
20 Then when Martha heard that Jesus was coming, she went and met him, but Mary stayed in the house.
Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
21 Therefore Martha said to Jesus, "Lord, if you would have been here, my brother would not have died.
Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
22 Even now I know that whatever you ask of God, God will give you."
Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
23 Jesus said to her, "Your brother will rise again."
Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
24 Martha said to him, "I know that he will rise again in the resurrection at the last day."
Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
25 Jesus said to her, "I am the resurrection and the life. He who believes in me will still live, even if he dies.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
26 And whoever lives and believes in me will never die. Do you believe this?" (aiōn g165)
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
27 She said to him, "Yes, Lord. I have come to believe that you are the Christ, the Son of God, he who comes into the world."
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
28 And when she had said this, she went away, and called Mary, her sister, secretly, saying, "The Teacher is here, and is calling you."
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
29 When she heard this, she arose quickly, and went to him.
Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
30 Now Jesus had not yet come into the village, but was still in the place where Martha met him.
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
31 Then the Judeans who were with her in the house, and were consoling her, when they saw Mary, that she rose up quickly and went out, followed her, supposing that she was going to the tomb to weep there.
Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
32 Therefore when Mary came to where Jesus was, and saw him, she fell down at his feet, saying to him, "Lord, if you would have been here, my brother would not have died."
Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
33 When Jesus therefore saw her weeping, and the Judeans weeping who came with her, he was deeply moved in spirit and was troubled,
Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
34 and said, "Where have you put him?" They told him, "Lord, come and see."
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
35 Jesus wept.
Yesu ya yi kuka.
36 The Judeans therefore said, "See how he loved him."
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
37 But some of them said, "Could not this man, who opened the eyes of him who was blind, have also kept this man from dying?"
Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
38 So Jesus, deeply moved again, came to the tomb. Now it was a cave, and a stone lay against it.
Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
39 Jesus said, "Take away the stone." Martha, the sister of the dead man, said to him, "Lord, by this time there is a stench, for he has been dead four days."
Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
40 Jesus said to her, "Did I not tell you that if you believed, you would see God's glory?"
Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
41 So they took away the stone. And Jesus lifted up his eyes, and said, "Father, I thank you that you listened to me.
Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
42 I know that you always listen to me, but because of the crowd that stands around I said this, that they may believe that you sent me."
Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
43 When he had said this, he shouted with a loud voice, "Lazarus, come out."
Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
44 The man who had died came out, bound hand and foot with wrappings, and his face was wrapped around with a cloth. Jesus said to them, "Free him, and let him go."
Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
45 Therefore many of the Judeans, who came to Mary and had seen the things which he did, believed in him.
Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
46 But some of them went away to the Pharisees, and told them the things which Jesus had done.
Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
47 The chief priests therefore and the Pharisees gathered a council, and said, "What are we doing? For this man does many signs.
Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
48 If we leave him alone like this, everyone will believe in him, and the Romans will come and take away both our place and our nation."
In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
49 But a certain one of them, Caiaphas, being high priest that year, said to them, "You know nothing at all,
Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
50 nor do you consider that it is advantageous for you that one man should die for the people, and that the whole nation not perish."
Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
51 Now he did not say this of himself, but being high priest that year, he prophesied that Jesus would die for the nation,
Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
52 and not for the nation only, but that he might also gather together into one the children of God who are scattered abroad.
ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
53 So from that day on they plotted to kill him.
Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
54 Jesus therefore walked no more openly among the Judeans, but departed from there into the country near the wilderness, to a city called Ephraim; and stayed there with his disciples.
Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
55 Now the Jewish Passover was near, and many went up from the country to Jerusalem before the Passover, to purify themselves.
Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
56 Then they sought for Jesus and spoke one with another, as they stood in the temple, "What do you think—that he is not coming to the feast at all?"
Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
57 Now the chief priests and the Pharisees had given orders that if anyone knew where he was, he should report it, that they might arrest him.
Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.

< John 11 >