< Yochanan 12 >

1 Then six days before the Passover, Jesus came to Bethany, where Lazarus was, whom Jesus raised from the dead.
Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu.
2 So they prepared a dinner for him there; and Martha served, but Lazarus was one of those reclining at the table with him.
Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.
3 Mary, therefore, took a pound of ointment of pure nard, very precious, and anointed the feet of Jesus, and wiped his feet with her hair. And the house was filled with the fragrance of the ointment.
Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.
4 Then Judas Iscariot, one of his disciples, who would betray him, said,
Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, “
5 "Why was this ointment not sold for three hundred denarii, and given to the poor?"
“Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?”
6 Now he said this, not because he cared for the poor, but because he was a thief, and having the money box, used to steal what was put into it.
Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
7 But Jesus said, "Leave her alone, that she may keep this for the day of my burial.
Yesu ya ce, “Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta.
8 For you always have the poor with you, but you do not always have me."
Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
9 A large crowd therefore of the Judeans learned that he was there, and they came, not for Jesus' sake only, but that they might see Lazarus also, whom he had raised from the dead.
To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu.
10 But the chief priests plotted to kill Lazarus also,
Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima;
11 because on account of him many of the Jewish people went away and believed in Jesus.
domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
12 On the next day the large crowd that had come to the feast heard that Jesus was coming to Jerusalem,
Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,
13 they took the branches of the palm trees, and went out to meet him, and were shouting, "Hosanna. Blessed is he who comes in the name of the Lord, the King of Israel."
Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, “Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
14 And Jesus, having found a young donkey, sat on it. As it is written,
Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,
15 "Do not be afraid, daughter of Zion. Look, your King comes, sitting on a donkey's colt."
“Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki”.
16 His disciples did not understand these things at first, but when Jesus was glorified, then they remembered that these things were written about him, and that they had done these things to him.
Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
17 The crowd therefore that was with him when he called Lazarus out of the tomb, and raised him from the dead, was testifying about it.
Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida.
18 For this cause also the crowd went and met him, because they heard that he had done this sign.
Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama.
19 The Pharisees therefore said among themselves, "See how you accomplish nothing. Look, the whole world has gone after him."
Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa “Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
20 Now there were certain Greeks among those that went up to worship at the feast.
Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin.
21 These, therefore, came to Philip, who was from Bethsaida of Galilee, and asked him, saying, "Sir, we want to see Jesus."
Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, “Mallam, muna so mu ga Yesu.
22 Philip came and told Andrew, and in turn, Andrew came with Philip, and they told Jesus.
Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
23 And Jesus answered them, "The time has come for the Son of Man to be glorified.
Yesu ya amsa masu ya ce, “sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum.
24 Truly, truly, I tell you, unless a grain of wheat falls into the earth and dies, it remains by itself alone. But if it dies, it bears much fruit.
Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
25 He who loves his life loses it, and he who hates his life in this world will keep it to everlasting life. (aiōnios g166)
Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. (aiōnios g166)
26 If anyone serves me, let him follow me; and where I am, there will my servant also be. If anyone serves me, the Father will honor him.
Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
27 "Now my soul is troubled. And what should I say? 'Father, save me from this hour?' But for this cause I came to this hour.
Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a.
28 Father, glorify your name." Then there came a voice out of the sky, saying, "I have both glorified it, and will glorify it again."
Uba, ka daukaka sunanka”. Sai wata murya daga sama ta ce, “Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi.
29 The crowd therefore, who stood by and heard it, said that it had thundered. Others said, "An angel has spoken to him."
Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, “Mala'ika ya yi magana da shi”.
30 Jesus answered, "This voice hasn't come for my sake, but for your sakes.
Yesu ya amsa ya ce, “wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku.”
31 Now is the judgment of this world. Now the prince of this world will be cast out.
Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
32 And I, when I am lifted up from the earth, will draw everyone to myself."
Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni”.
33 But he said this, signifying by what kind of death he should die.
Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
34 The crowd answered him, "We have heard out of the law that the Messiah remains forever. Then how can you say, 'The Son of Man must be lifted up?' Who is this Son of Man?" (aiōn g165)
Taro suka amsa masa cewa, “Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?” (aiōn g165)
35 Jesus therefore said to them, "Yet a little while the light is with you. Walk while you have the light, that darkness does not overtake you. He who walks in the darkness does not know where he is going.
Yesu ya ce masu, “Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba.
36 While you have the light, believe in the light, that you may become children of light." Jesus said these things, and he departed and hid himself from them.
Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske”. Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
37 But though he had done so many signs before them, yet they did not believe in him,
Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba.
38 that the word of Isaiah the prophet might be fulfilled, which he spoke, "Lord, who has believed our report, and to whom has the arm of the Lord been revealed?"
Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
39 For this cause they could not believe, for Isaiah said again,
Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa,
40 He has blinded their eyes and hardened their heart, lest they should see with their eyes, and understand with their heart, and turn, and I would heal them.
ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
41 Isaiah said these things because he saw his glory, and spoke of him.
Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi.
42 Nevertheless even of the rulers many believed in him, but because of the Pharisees they did not confess it, so that they would not be put out of the synagogue,
Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a.
43 for they loved praise from people more than praise from God.
Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
44 Then Jesus shouted out and said, "Whoever believes in me, believes not in me, but in him who sent me.
Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, “Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni,
45 And he who sees me sees him who sent me.
kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
46 I have come as a light into the world, that whoever believes in me may not remain in the darkness.
Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba.
47 And if anyone hears my words and does not keep them, I do not judge him. For I came not to judge the world, but to save the world.
Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
48 He who rejects me, and does not accept my words, has one who judges him. The word that I spoke will judge him on the last day.
Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe.
49 For I spoke not from myself, but the Father who sent me, he gave me a commandment, what I should say, and what I should speak.
Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi.
50 I know that his commandment is everlasting life. The things therefore which I speak, even as the Father has said to me, so I speak." (aiōnios g166)
Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi.” (aiōnios g166)

< Yochanan 12 >