< Hebrews 1 >

1 God, having in the past spoken to the fathers through the prophets at many times and in various ways,
A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
2 in these last days has spoken to us by a Son, whom he appointed heir of all things, through whom also he made the ages. (aiōn g165)
Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
3 He is the radiance of his glory, the very image of his substance, and upholding all things by the word of his power, when he had made purification for sins, sat down on the right hand of the Majesty on high;
Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
4 having become so much better than the angels, as he has inherited a more excellent name than they have.
Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
5 For to which of the angels did he say at any time, "You are my Son. Today I have become your Father"? And again, "I will be his Father, and he will be my Son"?
Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
6 And again, when he brings in the firstborn into the world he says, "Let all the angels of God worship him."
Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
7 Of the angels he says, "Who makes his angels winds, and his servants a flame of fire."
A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
8 But of the Son he says, "Your throne, O God, is forever and ever, and the righteous scepter is the scepter of your Kingdom. (aiōn g165)
A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn g165)
9 You have loved righteousness, and hated iniquity; therefore God, your God, has anointed you with the oil of gladness above your companions."
Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
10 And, "In the beginning, Lord, you established the foundation of the earth. The heavens are the works of your hands.
“Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
11 They will perish, but you remain; and they will all wear out like a garment.
Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
12 As a cloak, you will roll them up, and like a garment they will be changed. But you remain the same, and your years will have no end."
Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
13 But which of the angels has he told at any time, "Sit at my right hand, until I make your enemies the footstool of your feet?"
Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
14 Are they not all ministering spirits, sent out to do service for the sake of those who will inherit salvation?
Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?

< Hebrews 1 >