< Galatians 2 >

1 Then after a period of fourteen years I went up again to Jerusalem with Barnabas, taking Titus also with me.
Bayan shekara goma sha huɗu sai na sāke haurawa zuwa Urushalima, a wannan lokaci na tafi tare da Barnabas. Na kuma ɗauki Titus muka tafi tare.
2 I went up by revelation, and I explained to them the gospel which I preach among those who are not Jewish, but privately before those who were respected, for fear that I might be running, or had run, in vain.
Na tafi ne bisa ga wani wahayi. Da na kai can, sai na bayyana musu bisharar da nake wa’azi a cikin Al’ummai. Na yi haka a keɓance a gaban waɗanda suke shugabanni, don tsoro kada gudun da nake yi, ko kuwa na riga na yi, yă zama a banza.
3 But not even Titus, who was with me, being a Greek, was compelled to be circumcised.
Amma ko Titus ma da yake tare da ni, ba a ce dole sai ya yi kaciya ba, ko da yake shi mutumin Al’ummai ne.
4 This was because of the false brothers secretly brought in, who stole in to spy out our liberty which we have in Messiah Jesus, that they might bring us into bondage;
Wannan zancen kaciya ya taso domin waɗansu’yan’uwan ƙarya sun shiga cikinmu domin su yi leƙe a kan’yancin da muke da shi a cikin Kiristi Yesu, su kuma mai da mu bayi.
5 to whom we gave no place in the way of subjection, not for an hour, that the truth of the gospel might continue with you.
Ba mu kuwa ba su zarafi ba ko kaɗan, don gaskiyar bishara ta ci gaba da kasance tare da ku.
6 But from those who were reputed to be important (whatever they were, it makes no difference to me; God shows no favoritism between people)—they, I say, who were respected imparted nothing to me,
Game da waɗanda aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne, ko wane ne su, duk ɗaya ne a wurina; gama Allah ba ya nuna bambanci, ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙara mini kome ba.
7 but to the contrary, when they saw that I had been entrusted with the gospel for the uncircumcision, even as Peter with the gospel for the circumcision
A maimakon haka, sun ga cewa an danƙa mini hakkin wa’azin bishara ga Al’ummai, kamar yadda aka danƙa wa Bitrus ga Yahudawa.
8 (for he who appointed Peter to be an apostle of the circumcision appointed me also to the non-Jews);
Gama Allah wanda ya yi aiki a cikin hidimar Bitrus a matsayin manzo ga Yahudawa, haka ma ya yi aiki a cikin hidimata a matsayin manzo ga Al’ummai.
9 and when they perceived the grace that was given to me, James and Cephas and John, they who were reputed to be pillars, gave to me and Barnabas the right hand of fellowship, that we should go to the non-Jews, and they to the circumcised.
Yaƙub, Bitrus da Yohanna waɗanda suke fitattun ginshiƙai, sun karɓe ni da Barnabas da hannu biyu biyu sa’ad da suka gane alherin da aka ba ni. Suka kuma yarda cewa ya kamata mu tafi wajen Al’ummai, su kuwa su tafi wajen Yahudawa.
10 They only asked us to remember the poor—which very thing I was also zealous to do.
Abin da dai suka roƙa shi ne ya kamata mu riƙa tuna da matalauta, abin nan da nake marmarin yi.
11 But when Cephas came to Antioch, I resisted him to his face, because he stood condemned.
Sa’ad da Bitrus ya zo Antiyok, na tsawata masa ido da ido don laifinsa a fili yake.
12 For before some people came from James, he ate with those who were not Jewish. But when they came, he drew back and separated himself, fearing those who were of the circumcision.
Kafin waɗansu mutane su zo daga wurin Yaƙub, yakan ci abinci tare da Al’ummai. Amma da suka iso, sai ya fara janyewa, ya kuma ware kansa daga wajen Al’ummai domin yana tsoron waɗanda suke ƙungiyar masu kaciya.
13 And the rest of the Jewish believers joined him in his hypocrisy; so that even Barnabas was carried away with their hypocrisy.
Sauran Yahudawa suka haɗa kai da shi a munafuncinsa har Barnabas ma ya bauɗe.
14 But when I saw that they did not walk uprightly according to the truth of the gospel, I said to Cephas before them all, "If you, being a Jew, live as the non-Jews do, and not as the Jews do, how can you compel the non-Jews to live as the Jews do?
Da na ga cewa ba sa yin daidai da gaskiyar bishara, sai na ce wa Bitrus a gabansu duka, “Kai mutumin Yahuda ne, duk da haka kana rayuwa kamar Ba’al’umme ba kamar mutumin Yahuda ba. To, yaya aka yi, kana tilasta Al’ummai su bi al’adun Yahudawa?
15 "We, being Jews by birth, and not non-Jewish sinners,
“Mu da muke Yahudawa ta wurin haihuwa ba Al’ummai masu zunubi ba,
16 yet knowing that no one is justified by the works of the law but through faith in Jesus (the) Messiah, even we believed in Messiah Jesus, that we might be justified by faith in Messiah, and not by the works of the law, because no flesh will be justified by the works of the law.
mun san cewa mutum ba ya samun kuɓuta ta wurin kiyaye Doka, sai dai ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu. Saboda haka, mu ma, muka sa bangaskiyarmu cikin Kiristi Yesu don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya cikin Kiristi ba ta wurin kiyaye Doka ba, domin ba wanda zai kuɓuta ta wurin bin Doka.
17 But if, while we sought to be justified in Messiah, we ourselves also were found sinners, is Messiah a servant of sin? Certainly not.
“In kuwa ya zama muna so mu sami zaman marasa laifi a gaban Allah ta wurin dogara ga Kiristi, sa’an nan an same mu mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, ko wannan zai nuna Kiristi yana ƙarfafa zunubi ke nan? A’a, ko kusa!
18 For if I build up again those things which I destroyed, I prove myself a law-breaker.
In na sāke gina abin da na rushe, na zama mai karyar Doka ke nan.
19 For I, through the law, died to the law, that I might live to God.
“Gama ta wurin Doka na mutu ga Doka saboda in rayu ga Allah.
20 I have been crucified with Messiah, and it is no longer I that live, but Messiah living in me. That life which I now live in the flesh, I live by faith in the Son of God, who loved me, and gave himself up for me.
An gicciye ni tare da Kiristi. Yanzu ba ni ne nake raye ba, Kiristi ne yake raye a cikina. Rayuwar da nake yi a jiki, ina rayuwa ce ta wurin bangaskiya cikin Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni ya kuma ba da kansa domina.
21 I do not make void the grace of God. For if righteousness is through the law, then Messiah died for nothing."
Ba na ajiyar alherin Allah a gefe, gama da a ce ana samun adalci ta wurin Doka, ai, da Kiristi ya mutu a banza ke nan!”

< Galatians 2 >