< Numbers 1 >

1 Jehovah spoke to Moses in the wilderness of Sinai, in the Tent of Meeting, on the first day of the second month, in the second year after they had come out of the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 "Take a census of all the congregation of the children of Israel, by their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, every male, one by one;
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 from twenty years old and upward, all who are able to go out to war in Israel. You and Aaron shall number them by their divisions.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 With you there shall be a man of every tribe; everyone head of his fathers' house.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 These are the names of the men who shall stand with you: Of Reuben: Elizur the son of Shedeur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Of Simeon: Shelumiel the son of Zurishaddai.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Of Judah: Nahshon the son of Amminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Of Issachar: Nethanel the son of Zuar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Of Zebulun: Eliab the son of Helon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Of the sons of Joseph: Of Ephraim: Elishama the son of Ammihud. Of Manasseh: Gamaliel the son of Pedahzur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Of Benjamin: Abidan the son of Gideoni.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Of Dan: Ahiezer the son of Ammishaddai.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Of Asher: Pagiel the son of Ochran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Of Gad: Eliasaph the son of Reuel.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Of Naphtali: Ahira the son of Enan."
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These are those who were called of the congregation, the leaders of the tribes of their fathers; they were the heads of the thousands of Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Moses and Aaron took these men who are mentioned by name.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 They assembled all the congregation together on the first day of the second month; and they declared their ancestry by their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, one by one.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 As Jehovah commanded Moses, so he numbered them in the wilderness of Sinai.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Now the descendants of Reuben, Israel's firstborn, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, one by one, every male from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 those who were numbered of them, of the tribe of Reuben, were forty-six thousand five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Of the descendants of Simeon, their generations, according to their families, by their fathers' houses, those who were numbered of it, according to the number of the names, one by one, every male from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 those who were numbered of them, of the tribe of Simeon, were fifty-nine thousand three hundred.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Of the descendants of Gad, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 those who were numbered of them, of the tribe of Gad, were forty-five thousand six hundred fifty.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Of the descendants of Judah, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 those who were numbered of them, of the tribe of Judah, were sixty-four thousand six hundred.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Of the descendants of Issachar, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 those who were numbered of them, of the tribe of Issachar, were fifty-four thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Of the descendants of Zebulun, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 those who were numbered of them, of the tribe of Zebulun, were fifty-seven thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Of the sons of Joseph, of the descendants of Ephraim, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 those who were numbered of them, of the tribe of Ephraim, were forty thousand five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Of the descendants of Manasseh, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 those who were numbered of them, of the tribe of Manasseh, were thirty-two thousand two hundred.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Of the descendants of Benjamin, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war;
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 those who were numbered of them, of the tribe of Benjamin, were thirty-five thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Of the descendants of Dan, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go forth to war;
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 those who were numbered of them, of the tribe of Dan, were sixty-two thousand seven hundred.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Of the descendants of Asher, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go forth to war;
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 those who were numbered of them, of the tribe of Asher, were forty-one thousand five hundred.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Of the descendants of Naphtali, their generations, according to their families, by their fathers' houses, according to the number of the names, from twenty years old and upward, all who were able to go forth to war;
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 those who were numbered of them, of the tribe of Naphtali, were fifty-three thousand four hundred.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These are those who were numbered, whom Moses and Aaron numbered, and the leaders of Israel, being twelve men; each representing his fathers' house.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 So all those who were numbered of the children of Israel by their fathers' houses, from twenty years old and upward, all who were able to go out to war in Israel;
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 even all those who were numbered were six hundred three thousand five hundred fifty.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Levites after the tribe of their fathers were not numbered among them.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 For Jehovah spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 "Only the tribe of Levi you shall not number, neither shall you take a census of them among the children of Israel;
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 but appoint the Levites over the Tabernacle of the Testimony, and over all its furnishings, and over all that belongs to it. They shall carry the tabernacle, and all its furnishings; and they shall take care of it, and shall camp around it.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 When the tabernacle is to move, the Levites shall take it down; and when the tabernacle is to be set up, the Levites shall set it up. The unauthorized person who comes near shall be put to death.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 The children of Israel shall pitch their tents, every man by his own camp, and every man by his own standard, according to their divisions.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But the Levites shall camp around the Tabernacle of the Testimony, that there may be no wrath on the congregation of the children of Israel: and the Levites shall be responsible for the Tabernacle of the Testimony."
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Thus the children of Israel did. According to all that Jehovah commanded Moses, so they did.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >