< Numbers 34 >

1 Jehovah spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 "Command the children of Israel, and tell them, 'When you come into the land of Canaan (this is the land that shall fall to you for an inheritance, even the land of Canaan according to its borders),
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 then your south quarter shall be from the wilderness of Zin along by the side of Edom, and your south border shall be from the end of the Salt Sea eastward;
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 and your border shall turn about southward of the ascent of Akrabbim, and pass along to Zin; and the goings out of it shall be southward of Kadesh Barnea; and it shall go forth to Hazar Addar, and pass along to Azmon;
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 and the border shall turn about from Azmon to the Wadi of Egypt, and the goings out of it shall be at the sea.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 "'For the western border, the Great Sea shall be a border to you; this shall be your west border.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 "'This shall be your north border: from the Great Sea you shall mark out for you Mount Hor;
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 from Mount Hor you shall mark out to Lebo Hamath; and the goings out of the border shall be at Zedad;
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 and the border shall go forth to Ziphron, and the goings out of it shall be at Hazar Enan: this shall be your north border.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 "'You shall mark out your east border from Hazar Enan to Shepham;
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 and the border shall go down from Shepham to Riblah, on the east side of Ain; and the border shall go down, and shall reach to the side of the sea of Kinnereth eastward;
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 and the border shall go down to the Jordan, and the goings out of it shall be at the Salt Sea. This shall be your land according to its borders around it.'"
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Moses commanded the children of Israel, saying, "This is the land which you shall inherit by lot, which Jehovah has commanded to give to the nine tribes, and to the half-tribe;
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 for the tribe of the people of Reuben according to their fathers' houses, and the tribe of the people of Gad according to their fathers' houses, have received, and the half-tribe of Manasseh have received, their inheritance:
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 the two tribes and the half-tribe have received their inheritance beyond the Jordan at Jericho eastward, toward the sunrise."
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Jehovah spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 "These are the names of the men who shall divide the land to you for inheritance: Eleazar the priest, and Joshua the son of Nun.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 You shall take one prince of every tribe, to divide the land for inheritance.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 These are the names of the men: Of the tribe of Judah, Caleb the son of Jephunneh.
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 Of the tribe of the people of Simeon, Shemuel the son of Ammihud.
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 Of the tribe of Benjamin, Elidad the son of Chislon.
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 Of the tribe of the people of Dan a prince, Bukki the son of Jogli.
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Of the people of Joseph: of the tribe of the people of Manasseh a prince, Hanniel the son of Ephod.
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 Of the tribe of the people of Ephraim a prince, Kemuel the son of Shiphtan.
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 Of the tribe of the people of Zebulun a prince, Elizaphan the son of Parnach.
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 Of the tribe of the people of Issachar a prince, Paltiel the son of Azzan.
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 Of the tribe of the people of Asher a prince, Ahihud the son of Shelomi.
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 Of the tribe of the people of Naphtali a prince, Pedahel the son of Ammihud."
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 These are they whom Jehovah commanded to divide the inheritance to the children of Israel in the land of Canaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Numbers 34 >