< Job 36 >

1 Elihu also continued, and said,
Elihu ya ci gaba,
2 "Bear with me a little, and I will show you; for I still have something to say on God's behalf.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will get my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For truly my words are not false. One who is perfect in knowledge is with you.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 "Look, God is mighty, and doesn't despise anyone. He is mighty in strength of understanding.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He doesn't preserve the life of the wicked, but gives to the afflicted their right.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He doesn't withdraw his eyes from the righteous, but with kings on the throne, he sets them forever, and they are exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 If they are bound in fetters, and are taken in the cords of afflictions,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 then he shows them their work, and their transgressions, that they have behaved themselves proudly.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 He also opens their ears to instruction, and commands that they return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they listen and serve him, they shall spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they do not listen, they shall perish by the sword; they shall die without knowledge.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 "But those who are godless in heart lay up anger. They do not cry for help when he binds them.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 They die in youth. Their life perishes among the unclean.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 He delivers the afflicted by their affliction, and opens their ear in oppression.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Yes, he would have allured you out of distress, into a broad place, where there is no restriction. That which is set on your table would be full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 "But you are full of the judgment of the wicked. Judgment and justice take hold of you.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Do not let riches entice you to wrath, neither let the great size of a bribe turn you aside.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Would your wealth sustain you in distress, or all the might of your strength?
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Do not desire the night, when people are cut off in their place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed, do not regard iniquity; for you have chosen this rather than affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Look, God is exalted in his power. Who is a teacher like him?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who has prescribed his way for him? Or who can say, 'You have committed unrighteousness?'
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 "Remember that you magnify his work, whereof men have sung.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All men have looked thereon. Man sees it afar off.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Look, God is great, and we do not know him. The number of his years is unsearchable.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 For he draws up the drops of water, which distill in rain from his vapor,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Which the skies pour down and which drop on humankind abundantly.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Yes, can any understand the spreading of the clouds, and the thunderings of his pavilion?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Look, he spreads his light around him. He covers the bottom of the sea.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For by these he judges the people. He gives food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 He covers his hands with the lightning, and commands it to strike the mark.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 Its noise tells about him, and the livestock also concerning the storm that comes up.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >