< Isaiah 60 >

1 "Arise, shine; for your light has come, and the glory of Jehovah has risen upon you.
“Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
2 For, look, darkness shall cover the earth, and gross darkness the peoples; but Jehovah will arise on you, and his glory shall be seen on you.
Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
3 Nations shall come to your light, and kings to the brightness of your rising.
Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
4 "Lift up your eyes all around, and see: they all gather themselves together, they come to you; your sons shall come from far, and your daughters shall be carried in the arms.
“Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
5 Then you shall see and be radiant, and your heart shall thrill and be enlarged; because the abundance of the sea shall be turned to you, the wealth of the nations shall come to you.
Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
6 The multitude of camels shall cover you, the dromedaries of Midian and Ephah; all they from Sheba shall come; they shall bring gold and frankincense, and shall proclaim the praises of Jehovah.
Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
7 All the flocks of Kedar shall be gathered together to you, the rams of Nebaioth shall minister to you; they shall come up with acceptance on my altar; and I will glorify the house of my glory.
Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
8 "Who are these who fly as a cloud, and as the doves to their windows?
“Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
9 Surely the islands shall wait for me, and the ships of Tarshish first, to bring your sons from far, their silver and their gold with them, for the name of Jehovah your God, and for the Holy One of Israel, because he has glorified you.
Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
10 "Foreigners shall build up your walls, and their kings shall minister to you: for in my wrath I struck you, but in my favor have I had mercy on you.
“Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
11 Your gates also shall be open continually; they shall not be shut day nor night; that men may bring to you the wealth of the nations, and their kings led captive.
Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
12 For that nation and kingdom that will not serve you shall perish; yes, those nations shall be utterly wasted.
Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
13 "The glory of Lebanon shall come to you, the fir tree, the pine, and the box tree together, to beautify the place of my sanctuary; and I will make the place of my feet glorious.
“Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
14 The sons of those who afflicted you shall come bending to you; and all those who despised you shall bow themselves down at the soles of your feet; and they shall call you The city of Jehovah, The Zion of the Holy One of Israel.
’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 "Whereas you have been forsaken and hated, so that no man passed through you, I will make you an everlasting excellency, a joy of many generations.
“Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
16 You shall also drink the milk of the nations, and shall nurse from royal breasts; and you shall know that I, Jehovah, am your Savior, and your Redeemer, the Mighty One of Jacob.
Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
17 For bronze I will bring gold, and for iron I will bring silver, and for wood bronze, and for stones iron. I will also make your officers peace, and righteousness your ruler.
A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
18 Violence shall no more be heard in your land, destruction nor calamity within your borders; but you shall call your walls Salvation, and your gates Praise.
Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
19 The sun will no longer be your light by day, nor will the moon shine for illumination at night; but Jehovah will be your everlasting light, and your God will be your glory.
Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
20 Your sun shall no more go down, neither shall your moon withdraw itself; for Jehovah will be your everlasting light, and the days of your mourning shall be ended.
Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
21 Your people also shall be all righteous; they shall inherit the land forever, the branch of my planting, the work of my hands, that I may be glorified.
Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
22 The little one shall become a thousand, and the small one a strong nation; I, Jehovah, will hasten it in its time."
Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”

< Isaiah 60 >