< Genesis 37 >

1 Jacob lived in the land where his father had sojourned, in the land of Canaan.
Yaƙub ya zauna a ƙasar da mahaifinsa ya zauna, wato, ƙasar Kan’ana.
2 These are the generations of Jacob. Joseph, being seventeen years old, tended the flock with his brothers; he was an assistant to the sons of Bilhah and Zilpah, his father's wives. And Joseph brought a bad report about them to their father.
Wannan shi ne labarin zuriyar Yaƙub. Yusuf, saurayi ne mai shekara goma sha bakwai. Shi da’yan’uwansa, wato,’ya’yan Bilha maza da kuma’ya’yan Zilfa maza, matan mahaifinsa suna kiwon garkuna tare. Sai Yusuf ya kawo wa mahaifinsu rahoto marar kyau game da’yan’uwansa.
3 Now Israel loved Joseph more than all his children, because he had been born to him in his old age. And he made a long ornamented robe for him.
Isra’ila dai ya fi ƙaunar Yusuf fiye da kowanne a cikin sauran’ya’yansa maza, gama an haifa masa shi a cikin tsufansa. Sai ya yi masa riga mai gwanin kyau.
4 His brothers saw that their father loved him more than all his brothers, and they hated him, and couldn't speak a kind word to him.
Sa’ad da’yan’uwansa suka ga cewa mahaifinsu ya fi ƙaunarsa fiye da kowanne daga cikinsu, sai suka ƙi jininsa, ba sa kuma maganar alheri da shi.
5 Now Joseph had a dream, and he told it to his brothers, and they hated him all the more.
Sai Yusuf ya yi mafarki, sa’ad da ya faɗa wa’yan’uwansa, suka ƙara ƙin jininsa.
6 He said to them, "Please listen to this dream I had:
Ya ce musu, “Ku saurari wannan mafarkin da na yi.
7 And look, we were binding sheaves in the field, and look, my sheaf arose and also stood upright. And look, your sheaves gathered around it and bowed down to my sheaf."
Muna daurin dammunan hatsi a gona, sai nan da nan damina ya tashi ya tsaya, yayinda dammunanku suka taru kewaye da nawa suka rusuna masa.”
8 Then his brothers said to him, "Will you indeed reign over us? Or will you indeed rule over us?" So they hated him all the more for his dreams and for what he said.
Sai’yan’uwansa suka ce masa, “Kana nufin za ka yi mulki a kanmu ke nan? Ko kuwa za ka zama sarki, a bisanmu?” Suka ƙara ƙin jininsa saboda mafarkinsa da kuma abin da ya faɗa.
9 And he had another dream, and told it to his father and to his brothers, and said, "Look, I had yet another dream, and look, the sun and the moon and eleven stars bowed down to me."
Sai Yusuf ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa’yan’uwansa. Ya ce, “Ku saurara, na sāke yin wani mafarki, a wannan lokaci, na ga rana da wata da taurari goma sha ɗaya suna rusuna mini.”
10 When he told it to his father and to his brothers, his father rebuked him, and said to him, "What is this dream that you had? Will I and your mother and your brothers indeed come and bow down to the ground in front of you?"
Sa’ad da ya faɗa wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa, sai mahaifinsa ya kwaɓe shi ya ce, “Wanne irin mafarki ne haka da ka yi? Kana nufin ni da mahaifiyarka da’yan’uwanka za mu zo gabanka mu rusuna maka?”
11 His brothers were jealous of him, but his father kept thinking about the matter.
’Yan’uwansa suka yi kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe batun nan a zuciya.
12 Now his brothers went to pasture their father's flock near Shechem.
To,’yan’uwansa suka tafi kiwon garkunan mahaifinsu kusa da Shekem.
13 And Israel said to Joseph, "Aren't your brothers pasturing the flock near Shechem? Come, and I will send you to them." And he said to him, "I am ready."
Sai Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Kamar yadda ka sani,’yan’uwanka suna kiwon garkuna kusa da Shekem. Zo, in aike ka gare su.” Ya ce, “To.”
14 So he said to him, "Go now, see whether it is well with your brothers and well with the flock, and report back to me." So he sent him from the Valley of Hebron, and he came to Shechem.
Saboda haka Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Jeka ka ga ko kome lafiya yake da’yan’uwanka da kuma garkunan, ka kawo mini labari.” Sa’an nan ya sallame shi daga Kwarin Hebron. Sa’ad da Yusuf ya kai Shekem,
15 And a man found him, and look, he was wandering in the field. And the man asked him, "What are you looking for?"
sai wani mutum ya same shi yana yawo a cikin jeji, sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?”
16 He said, "I am looking for my brothers. Tell me, please, where they are pasturing the flock."
Yusuf ya amsa ya ce, “Ina neman’yan’uwana ne. Za ka iya faɗa mini inda suke kiwon garkunansu?”
17 The man said, "They have left here, for I heard them say, 'Let us go to Dothan.'" So Joseph went after his brothers, and found them in Dothan.
Mutumin ya amsa, “Sun yi gaba daga nan. Na ji su suna cewa, ‘Bari mu je Dotan.’” Saboda haka Yusuf ya bi bayan’yan’uwansa, ya kuwa same su kusa da Dotan.
18 Now they saw him in the distance, and before he reached them they plotted against him to kill him.
Amma da suka gan shi daga nesa, kafin yă kai wurinsu, sai suka ƙulla su kashe shi.
19 And they said to one another, "Look, this dreamer is coming.
Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can zuwa!
20 Come now, and let's kill him and throw him into one of the cisterns, and we will say that a vicious animal has devoured him. Then we will see what will become of his dreams."
Ku zo mu kashe shi mu kuma jefa shi a ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, mu ce mugun naman jeji ya cinye shi. Mu ga yadda mafarkinsa zai cika.”
21 But Reuben heard it, and delivered him out of their hands, and said, "Let's not take his life."
Sa’ad da Ruben ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă cece shi daga hannuwansu. Ya ce, “Kada mu ɗauki ransa.
22 Reuben said to them, "Shed no blood. Throw him into this pit that is in the wilderness, but lay no hand on him"—that he might deliver him out of their hands, to restore him to his father.
Kada mu zub da wani jini. Mu dai jefa shi cikin wannan rijiya a nan cikin hamada, amma kada mu sa hannu a kansa.” Ruben ya faɗa wannan ne don yă cece shi daga gare su, yă kuma mai da shi ga mahaifinsa.
23 It happened, when Joseph came to his brothers, they stripped Joseph of his robe, the long ornamented robe that he was wearing.
Saboda haka sa’ad da Yusuf ya zo wurin’yan’uwansa, sai suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai gwanin kyau da ya sa,
24 And they took him and threw him into the cistern. (Now the pit was empty. There was no water in it.)
suka kuma ɗauke shi suka jefa a cikin rijiya. To, rijiyar wofi ce, babu ruwa a ciki.
25 Then they sat down to eat a meal. And they looked up, and look, a caravan of Ishmaelites was coming from Gilead, with their camels bearing aromatic gum and balm and myrrh on their way to carry them down to Egypt.
Da suka zauna don cin abinci, sai suka tā da idanu, suka ga ayarin mutanen Ishmayel suna zuwa daga Gileyad. An yi wa raƙumansu labtu da kayan yaji da na ƙanshi, suna kan hanyarsu za su Masar.
26 Then Judah said to his brothers, "What profit is it if we kill our brother and conceal his blood?
Yahuda ya ce wa’yan’uwansa, “Me zai amfane mu in muka kashe ɗan’uwanmu muka ɓoye jininsa?
27 Come, and let's sell him to the Ishmaelites, and not lay a hand on him, for he is our brother, our flesh." And his brothers agreed.
Ku zo, mu sayar da shi wa mutanen Ishmayelawan nan, kada mu sa hannuwanmu a kansa; ban da haka ma, shi ɗan’uwanmu ne, jiki da jininmu.” Sai’yan’uwansa suka yarda.
28 So the Midianites merchants passed by, and they pulled him up and lifted Joseph out of the cistern, and sold Joseph to the Ishmaelites for twenty pieces of silver. And they brought Joseph to Egypt.
Saboda haka sa’ad da Fataken Midiyawa suka iso, sai’yan’uwansa suka ja Yusuf daga rijiyar, suka sayar da shi a bakin shekel ashirin na azurfa wa mutanen Ishmayel, waɗanda suka ɗauke shi zuwa Masar.
29 And Reuben returned to the cistern and saw that Joseph wasn't in the cistern; and he tore his clothes.
Sa’ad da Ruben ya dawo wurin rijiyar, sai ya tarar cewa Yusuf ba ya can, sai ya kyakkece tufafinsa.
30 He went back to his brothers and said, "The boy is gone. Now, what am I to do?"
Ya koma wurin’yan’uwansa ya ce, “Yaron ba ya can! Ina zan bi yanzu?”
31 They took Joseph's robe and killed a male goat and dipped the robe in the blood.
Sai suka ɗauki rigar Yusuf, suka yanka akuya suka tsoma rigar a cikin jinin.
32 And they sent the long ornamented robe and they brought it to their father, and said, "We found this. Please examine it to see whether it is your son's robe or not."
Suka ɗauki rigan nan mai gwanin kyau, suka kawo wa mahaifinsu suka ce, “Mun sami wannan. Ka bincika shi ka gani ko rigar ɗanka ne.”
33 And he recognized it, and said, "It is my son's robe. A vicious animal has devoured him. Joseph is without doubt torn to pieces."
Ya gane shi, sai ya ce, “Rigar ɗana ne! Waɗansu mugayen namun jeji sun cinye shi. Tabbatacce an yayyaga Yusuf.”
34 Then Jacob tore his clothes, and put sackcloth around his waist, and mourned for his son many days.
Sa’an nan Yaƙub ya kyakkece tufafinsa, ya sa tufafin makoki, ya kuma yi makoki domin ɗansa kwanaki masu yawa.
35 All his sons and all his daughters rose up to comfort him, but he refused to be comforted. And he said, "Indeed, I will go down to Sheol to my son mourning." And his father wept for him. (Sheol h7585)
Dukan’ya’yansa maza da mata, suka zo don su ta’azantar da shi, amma ya ƙi yă ta’azantu. Ya ce, “A’a, cikin makoki zan gangara zuwa kabari wurin ɗana.” Saboda haka, mahaifin Yusuf ya yi kuka saboda shi. (Sheol h7585)
36 Now the Midianites sold him into Egypt to Potiphar, an officer of Pharaoh, the captain of the guard.
Ana cikin haka, Midiyawa suka sayar da Yusuf a Masar wa Fotifar, ɗaya daga cikin shugabannin’yan gadin fadar Fir’auna.

< Genesis 37 >