< Ephesians 1 >

1 Paul, an apostle of Christ Jesus through the will of God, to the saints (in Ephesus) who are faithful in Christ Jesus:
Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
2 Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
3 Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who has blessed us with every spiritual blessing in the heavenly places in Christ;
Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
4 even as he chose us in him before the foundation of the world, that we would be holy and without blemish before him in love;
Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
5 having predestined us for adoption as sons through Jesus Christ to himself, according to the good pleasure of his desire,
A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
6 to the praise of the glory of his grace, which he freely bestowed on us in the Beloved One,
Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
7 in whom we have our redemption through his blood, the forgiveness of our trespasses, according to the riches of his grace,
A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
8 which he made to abound toward us in all wisdom and prudence,
wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
9 making known to us the mystery of his will, according to his good pleasure which he purposed in him
Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
10 to an administration of the fullness of the times, to sum up all things in Christ, the things in the heavens, and the things on the earth, in him;
Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
11 in whom also we were assigned an inheritance, having been foreordained according to the purpose of him who works all things after the counsel of his will;
A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
12 to the end that we should be to the praise of his glory, we who had before hoped in Christ:
Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
13 in whom you also, having heard the word of the truth, the Good News of your salvation, —in whom, having also believed, you were sealed with the Holy Spirit of promise,
An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
14 who is a pledge of our inheritance, to the redemption of God's own possession, to the praise of his glory.
Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
15 For this cause I also, having heard of the faith in the Lord Jesus which is among you, and the love which you have toward all the saints,
Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
16 do not cease to give thanks for you, making mention of you in my prayers,
ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
17 that the God of our Lord Jesus Christ, the Father of glory, may give to you a spirit of wisdom and revelation in the knowledge of him;
Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
18 having the eyes of your heart enlightened, that you may know what is the hope of his calling, and what are the riches of the glory of his inheritance in the saints,
Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
19 and what is the exceeding greatness of his power toward us who believe, according to that working of the strength of his might
Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
20 which he worked in Christ, when he raised him from the dead, and made him to sit at his right hand in the heavenly places,
da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
21 far above all rule, and authority, and power, and dominion, and every name that is named, not only in this age, but also in that which is to come. (aiōn g165)
Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
22 He put all things under his feet, and gave him to be head over all things for the church,
Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
23 which is his body, the fullness of him who fills all in all.
Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.

< Ephesians 1 >