< Mark 10 >

1 He arose from there and came into the borders of Yehuda and beyond the Yurdinan. Crowds came together to him again. As he usually did, he was again teaching them.
Yesu ya bar wannan wurin, ya tafi yankin Yahudiya, wajen hayin kogin Urdun. Sai jama'a suka je wurinsa. Ya ci gaba da koya masu, kamar yadda ya zama al'adarsa.
2 Pharisees came to him testing him, and asked him, "Is it lawful for a man to divorce his wife?"
Sai Farisawa su ka zo wurinsa, su ka ce, '' dai dai ne mutum ya saki matarsa?'' Wannan tambaya sun yi ta ne domin su gwada shi.
3 He answered, "What did Mushe command you?"
Ya amsa ya ce, menene Musa ya umarce ku?
4 They said, "Mushe allowed a certificate of divorce to be written, and to divorce her."
Suka ce, ''Musa ya yarda mutum ya rubuta takardar saki ga matarsa, ya sallameta ta fita.''
5 But Yeshua said to them, "Because of your hardness of heart, he wrote you this commandment.
“Domin taurin zuciyarku ne ya rubuta maku wannan dokar,” Yesu ya ce masu.
6 But from the beginning of the creation, he made them male and female.
Amman tun daga farkon halitta, 'Allah ya halicci namiji da ta mata.'
7 For this cause a man will leave his father and mother, and will join to his wife,
Domin wannan dalilin ne mutum zai rabu mahaifinsa da mahaifiyarsa ya mannewa matarsa.
8 and the two will become one flesh, so that they are no longer two, but one flesh.
Su biyu kuwa sun zama jiki daya, ba biyu ba,
9 What therefore God has joined together, let no one separate."
Saboda haka abinda Allah ya hada kada mutum ya raba.”
10 In the house, the disciples asked him again about the same matter.
Lokacin da suke cikin gida, sai almajiransa suka sake tambayarsa akan wannan magana.
11 He said to them, "Whoever divorces his wife, and marries another, commits adultery against her.
Ya ce da su. Dukan wanda ya saki matarsa ya kuma auro wata matar yayi zina da ita kenan.
12 If she herself divorces her husband, and marries another, she commits adultery."
Haka nan duk matar da ta saki mijinta ta auri wani ta yi zina da shi kenan.”
13 They were bringing to him little children, that he should touch them, but the disciples rebuked them.
Mutane suka kawo masa 'ya'yansu kanana don ya taba su, sai almajiransa suka kwabe su.
14 But when Yeshua saw it, he was moved with indignation, and said to them, "Allow the little children to come to me. Do not forbid them, for the Kingdom of God belongs to such as these.
Da Yesu ya gani, ya ji haushi, ya ce masu. Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su domin mulkin Allah na irinsu ne.
15 Truly I tell you, whoever will not receive the Kingdom of God like a little child, he will in no way enter into it."
Gaskiya na ke fada maku duk mutumin da bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, babu shakka ba zai shiga mulkin Allah ba.
16 And he took them in his arms, laying his hands on them, and blessed them.
Sai ya rungume su ya sa masu albarka.
17 As he was going out into the way, one ran to him, knelt before him, and asked him, "Good Teacher, what must I do that I may inherit everlasting life?" (aiōnios g166)
Lokacin da ya fara tafiya, sai wani mutum ya rugo wurinsa, ya durkusa a gabansa. Ya tambaye shi, yace ya ''Malam managarci, me zan yi domin in sami rai na har abada?'' (aiōnios g166)
18 Yeshua said to him, "Why do you call me good? No one is good except one—God.
Amma Yesu ya ce masa. Don me ka ke kira na managarci? Babu wani managarci sai dai Allah kadai.
19 You know the commandments: 'Do not commit adultery,' 'Do not murder,' 'Do not steal,' 'Do not give false testimony,' 'Do not defraud,' 'Honor your father and mother.'"
Kasan dokokin. Kada ka yi kisan kai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar zur, kada ka yi zamba, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
20 And he said to him, "Teacher, I have kept all these things from my youth."
Sai mutumin ya ce masa Malam ai na kiyayye duk wadannan abubuwa tun ina yaro.
21 Yeshua looking at him loved him, and said to him, "One thing you lack. Go, sell whatever you have, and give to the poor, and you will have treasure in heaven; and come, follow me, taking up the cross."
Yesu ya dube shi duban kauna ya ce masa. Abu daya ka rasa. Shi ne ka je ka sayar da duk mallakarka ka ba mabukata, za ka sami wadata a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.
22 But his face fell at that saying, and he went away sorrowful, for he was one who had great possessions.
Da ya ji haka sai ransa ya baci, ya tafi yana bakin ciki, don shi mai arziki ne kwarai.
23 Yeshua looked around, and said to his disciples, "How difficult it is for those who have riches to enter into the Kingdom of God."
Yesu ya dubi almajiransa ya ce. ''Yana da wuya masu arziki su shiga mulkin Allah!''
24 The disciples were amazed at his words. But Yeshua answered again and said to them, "Children, how hard it is for those who trust in riches to enter the kingdom of God.
Almajiransa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ce masu, ya ku ya'ya'na yana da wuya kamar me a shiga mulkin Allah.
25 It is easier for a camel to go through a needle's eye than for a rich person to enter into the Kingdom of God."
Zai zama da sauki ga rakumi yabi ta kafar allura da mai arziki ya shiga mulkin Allah.
26 They were exceedingly astonished, saying to him, "Then who can be saved?"
Sai suka cika da mamaki sosai, su kace wa juna, ''to idan haka ne wanene zai iya tsira kenan?''
27 Yeshua, looking at them, said, "With humans it is impossible, but not with God, for all things are possible with God."
Yesu ya dube su ya ce masu. Ga mutane a bu ne mai wuyar gaske, amma a wurin Allah komai yiwuwa ne.
28 Kipha began to tell him, "Look, we have left everything, and have followed you."
Bitrus ya ce masa, ''to gashi mu mun bar kome, mun bika''.
29 Yeshua said, "Truly I tell you, there is no one who has left house, or brothers, or sisters, or mother, or father, or children, or land, for my sake, and for the sake of the Good News,
Yesu ya ce. Gaskiya na ke fada maku, babu wanda zai bar gidansa, da yan'uwansa maza da mata, da mahaifiya ko mahaifi, ko 'ya'ya ko gona, saboda da ni da kuma bishara,
30 but he will receive one hundred times more now in this time, houses, brothers, sisters, mothers, children, and land, with persecutions; and in the age to come, everlasting life. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa'annan ya rasa samun nikinsu dari a zamanin yanzu, na gidaje, da yan'uwa mata da maza' da iyaye mata da 'ya'ya da gonaki, game da tsanani, a duniya mai zuw kuma ya sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 But many who are first will be last; and the last first."
Da yawa wadanda suke na farko za su koma na karshe, na karshe kuma za su zama na farko.
32 They were on the way, going up to Urishlim; and Yeshua was going in front of them, and they were amazed; and those who followed were afraid. He again took the twelve, and began to tell them the things that were going to happen to him.
Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa na gabansu. Almajiransa sun yi mamaki, mutane da ke biye da su kuwa sun tsorata. Yesu kuwa ya sake kebe sha biyun nan, ya fara fada masu abin da zai same shi.
33 "Look, we are going up to Urishlim. The Son of Man will be delivered to the chief priests and the scribes. They will condemn him to death, and will deliver him to foreigners.
“Kun ga, za mu Urushalima za a bada Dan mutum ga manyan Firistoci da malan Attaura, za su kuma yi masa hukuncin kisa su kuma bada shi ga al'ummai.
34 They will mock him, spit on him, scourge him, and kill him. After three days he will rise again."
Za su yi masa ba a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuwa zai tashi.”
35 Yaquv and Yukhanan, the sons of Zabedai, came near to him, and said to him, "Teacher, we want you to do for us whatever we will ask."
Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka zo wurin sa, suka ce, ''Malam muna so kayi mana duk abin da mu ka roke ka''
36 He said to them, "What do you want me to do for you?"
Ya ce masu. ''Me ku ke so in yi maku?''
37 They said to him, "Grant to us that we may sit, one at your right hand, and one at your left hand, in your glory."
Suka ce, ''ka yardar mana, a ranar daukakarka, mu zauna daya a damanka, daya kuma a hagunka.''
38 But Yeshua said to them, "You do not know what you are asking. Are you able to drink the cup that I drink, or to be baptized with the baptism that I am baptized with?"
Yesu ya ce masu. ''Ba ku san abinda ku ke roka ba. Kwa iya sha daga kokon da zan sha? Ko kuma za a yi maku baftismar da za a yi mani?''
39 And they said to him, "We are able." And Yeshua said to them, "You will drink the cup I drink, and you will be baptized with the baptism that I am baptized with;
Suka fada masa, ''Zamu iya.'' Yesu ya ce masu, '' kokon da zan sha, da shi zaku sha, baftismar da za ayi mani kuma da ita za a yi maku.''
40 but to sit at my right hand and at my left hand is not mine to give, but for whom it has been prepared."
Amma zama a damata, ko a haguna, ba na wa ba ne da zan bayar, ai na wadanda a ka shiryawa ne.”
41 When the ten heard it, they began to be indignant towards Yaquv and Yukhanan.
Da sauran almajiran nan goma suka ji, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya.
42 Yeshua summoned them, and said to them, "You know that they who are recognized as rulers over the nations lord it over them, and their great ones exercise authority over them.
Yesu kuma ya kira su wurinsa ya ce masu, '' kun sani wadanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna masu iko, hakimansu kuma sukan gasa masu iko.
43 But it will not be so among you, but whoever wants to become great among you must be your servant.
Amma ba haka zai kasance a tsakaninku ba. Duk wanda ya ke son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku.
44 And whoever wants to be first among you must be slave of all.
Duk wanda ya ke so ya shugabance ku lalle ne ya zama bawan kowa.
45 For the Son of Man also did not come to be served, but to serve, and to give his life as a ransom for many."
Saboda haka ne Dan mutum ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi yayi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda da mutane da yawa.”
46 They came to Irikhu. As he went out from Irikhu, with his disciples and a large crowd, Timai bar Timai, a blind beggar, was sitting by the road.
Sa'adda suka iso Yariko, yana fita daga Yariko kenan, shi da almajiransa, da wani babban taro, sai ga wani makaho mai bara, mai suna Bartimawas dan Timawas yana zaune a gefen hanya.
47 When he heard that it was Yeshua the Natsraya, he began to cry out, and say, "Yeshua, Son of Dawid, have mercy on me."
Da ya ji Yesu Banazare ne, ya fara daga murya yana cewa, ''Ya Yesu, Dan Dauda, kaji tausayina''
48 Many rebuked him, that he should be quiet, but he shouted all the louder, "Son of Dawid, have mercy on me."
Mutane da yawa suka kwabe shi, cewa yayi shiru. Sai ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, Ya Dan Dauda ka yi mani jinkai, ka ji tausayina!”
49 Yeshua stood still, and said, "Call him." They called the blind man, saying to him, "Cheer up. Get up. He is calling you."
Yesu ya tsaya ya ce, ku kirawo shi. Su kuwa suka kirawo makahon suka ce masa. ''Albishrinka, ta so! Yana kiranka.''
50 He, casting away his coat, jumped up, and came to Yeshua.
Makahon ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu.
51 Yeshua asked him, "What do you want me to do for you?" The blind man said to him, "Rabbuli, that I may see again."
Yesu ya tambaye shi, ya ce, '' me ka ke so in yi maka?'' Makahon ya ce, ''Malam in sami gani.''
52 Yeshua said to him, "Go your way. Your faith has made you well." And immediately he received his sight, and followed him on the road.
Yesu ya ce masa. ''Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.'' Nan take idanunsa suka bude, ya bi Yesu, suka tafi tare.

< Mark 10 >