< Luke 3 >

1 Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Yehuda, and Herod being tetrarch of Galila, and his brother Philipus tetrarch of the region of Ituraea and Trachona, and Lusania tetrarch of Avilina,
A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
2 in the high priesthood of Khanan and Qayapha, the word of God came to Yukhanan, the son of Zekharya, in the wilderness.
kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
3 He came into all the region around the Yurdinan, preaching a baptism of repentance for forgiveness of sins.
Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4 As it is written in the scroll of the words of Eshaya the prophet, "The voice of one crying in the wilderness, 'Prepare the way of the Lord. Make his roads straight.
Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5 Every valley will be filled, and every mountain and hill will be made low, and the crooked will be made straight, and the rough ways smooth.
Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
6 And all humanity will see the salvation of God.'"
kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7 He said therefore to the crowds who went out to be baptized by him, "You offspring of vipers, who warned you to flee from the wrath to come?
Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Bring forth therefore fruits worthy of repentance, and do not begin to say among yourselves, 'We have Avraham for our father;' for I tell you that God is able to raise up children to Avraham from these stones.
Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9 Even now the axe also lies at the root of the trees. Every tree therefore that does not bring forth good fruit is cut down, and thrown into the fire."
Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10 The crowds asked him, "What then must we do?"
Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11 He answered them, "He who has two coats, let him give to him who has none. He who has food, let him do likewise."
Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12 Tax collectors also came to be baptized, and they said to him, "Teacher, what must we do?"
Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13 He said to them, "Collect no more than that which is appointed to you."
Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
14 Soldiers also asked him, saying, "What about us? What must we do?" He said to them, "Extort from no one by violence, neither accuse anyone wrongfully. Be content with your wages."
Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
15 As the people were in expectation, and all were wondering in their hearts concerning Yukhanan, whether perhaps he was the Meshikha,
Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
16 Yukhanan answered them all, "I indeed baptize you with water, but he comes who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to loosen. He will baptize you with the Rukha d'Qudsha and with fire,
Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17 whose winnowing fork is in his hand, to clear his threshing floor, and to gather the wheat into his barn; but he will burn up the chaff with unquenchable fire."
Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18 Then with many other exhortations he preached good news to the people,
Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
19 but Herod the tetrarch, being reproved by him for Herodia, his brother's wife, and for all the evil things which Herod had done,
Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
20 added this also to them all, that he shut up Yukhanan in prison.
Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21 Now it happened, when all the people were baptized, Yeshua also had been baptized, and was praying. The sky was opened,
Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
22 and the Rukha d'Qudsha descended in a bodily form as a dove on him; and a voice came out of the sky, saying "You are my beloved Son. In you I am well pleased."
kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
23 When he began, Yeshua was about thirty years old, being the son, as was supposed, of Yauseph, of Heli,
Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
24 of Matathath, of Lewi, of Malki, of Yanai, of Yauseph,
dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25 of Matta, of Amus, of Nakhum, of Khesli, of Nagi,
dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
26 of Math, of Matath, of Shamey, of Yauseph, of Yehudah,
dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27 of Yoanan, of Rhesa, of Zurbabel, of Shelatheil, of Niri,
dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
28 of Malki, of Adi, of Cosam, of Elmodam, of Ear,
dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
29 of Yausi, of Eliazar, of Yuram, of Mathitha, of Lewi,
dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30 of Shimon, of Yehudah, of Yauseph, of Yunan, of Eliyaqim,
dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
31 of Melea, of Mani, of Mattha, of Nathan, of Dawid,
dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
32 of Ishai, of Euvid, of Baaz, of Salmun, of Nakhshun,
dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33 of Aminadav, of Aram, of Khesrun, of Partz, of Yehudah,
dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
34 of Yaquv, of Iskhaq, of Avraham, of Tarakh, of Nakhur,
dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
35 of Sarug, of Aruw, of Palag, of Auvar, of Shelakh,
dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36 of Qeynan, of Arphakshad, of Shim, of Nukh, of Lamek,
dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
37 of Mathushelakh, of Khenuk, of Yared, of Mahlalayel, of Qeynan,
dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
38 of Anush, of Shaeth, of Adom, of God.
dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.

< Luke 3 >