< John 9 >

1 And as he passed by, he saw a man blind from birth.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 And his disciples asked him, "Rabbi, who sinned, this man or his parents, that he was born blind?"
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Yeshua answered, "Neither did this man sin, nor his parents; but, that the works of God might be revealed in him.
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 We must work the works of him who sent me, while it is day. The night is coming, when no one can work.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 While I am in the world, I am the light of the world."
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 When he had said this, he spat on the ground, made mud with the saliva, anointed the blind man's eyes with the mud,
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 and said to him, "Go, wash in the pool of Shilukha" (which means "Sent"). So he went away, washed, and came back seeing.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 The neighbors therefore, and those who saw that he was a beggar before, said, "Is this not the one who used to sit and beg?"
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Some said, "It is he." Others said, "He looks like him." He said, "I am he."
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 They therefore were asking him, "How were your eyes opened?"
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 He answered, "A man called Yeshua made mud, anointed my eyes, and said to me, 'Go to Shilukha, and wash.' So I went away and washed, and I received sight."
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 Then they asked him, "Where is he?" He said, "I do not know."
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 They brought him who had been blind to the Pharisees.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 Now it was a Sabbath on the day when Yeshua made the mud and opened his eyes.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 Again therefore the Pharisees also asked him how he received his sight. He said to them, "He put mud on my eyes, I washed, and I see."
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Some therefore of the Pharisees said, "This man is not from God, because he does not keep the Sabbath." Others said, "How can a man who is a sinner do such signs?" There was division among them.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 Therefore they asked the blind man again, "What do you say about him, because he opened your eyes?" He said, "He is a prophet."
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 The Jewish leaders therefore did not believe concerning him, that he had been blind, and had received his sight, until they called the parents of him who had received his sight,
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 and asked them, "Is this your son, who you say was born blind? How then does he now see?"
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 His parents answered them, "We know that this is our son, and that he was born blind;
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 but how he now sees, we do not know; or who opened his eyes, we do not know. He is of age. Ask him. He will speak for himself."
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 His parents said these things because they feared the Jewish leaders; for the Jewish leaders had already agreed that if anyone would confess him as the Meshikha, he would be put out of the synagogue.
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 Therefore his parents said, "He is of age. Ask him."
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 So they called the man who was blind a second time, and said to him, "Give glory to God. We know that this man is a sinner."
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 He therefore answered, "I do not know if he is a sinner. One thing I do know: that though I was blind, now I see."
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 They said to him, "What did he do to you? How did he open your eyes?"
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 He answered them, "I told you already, and you did not listen. Why do you want to hear it again? You do not also want to become his disciples, do you?"
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 They insulted him and said, "You are his disciple, but we are disciples of Mushe.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 We know that God has spoken to Mushe. But as for this man, we do not know where he comes from."
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 The man answered them, "How amazing. You do not know where he comes from, yet he opened my eyes.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 We know that God does not listen to sinners, but if anyone is a worshipper of God, and does his will, he listens to him.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Since the world began it has never been heard of that anyone opened the eyes of someone born blind. (aiōn g165)
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn g165)
33 If this man were not from God, he could do nothing."
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 They answered him, "You were altogether born in sins, and do you teach us?" They threw him out.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Yeshua heard that they had thrown him out, and finding him, he said, "Do you believe in the Son of Man?"
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 He answered, "Who is he, Lord, that I may believe in him?"
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Yeshua said to him, "You have both seen him, and it is he who speaks with you."
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 He said, "Lord, I believe." and he worshiped him.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Yeshua said, "I came into this world for judgment, that those who do not see may see; and that those who see may become blind."
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Those of the Pharisees who were with him heard these things, and said to him, "Are we also blind?"
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Yeshua said to them, "If you were blind, you would have no sin; but since you say, 'We see,' your sin remains.
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

< John 9 >