< Hebrews 7 >

1 For this Malki-Zedeq, king of Shalim, priest of God Most High, who met Avraham returning from the slaughter of the kings and blessed him,
Wannan ne Malkisadak, sarkin Salem, firist na Allah Madaukaki, wanda ya gamu da Ibrahim na dawowa daga yaki da wasu sarakuna ya kuma albarkace shi.
2 to whom also Avraham divided "a tenth part of everything" (being first, by interpretation, king of righteousness, and then also king of Shalim, which is king of peace;
Ibrahim ya ba shi ushirin dukkan ganimar da ya samu. Sunansa,” Malkisadak,” ma'anar itace, “Sarkin adalci,” haka ma, “sarkin salem,” ma'anar iitace,” Sarkin salama,”
3 without father, without mother, without genealogy, having neither beginning of days nor end of life, but made like the Son of God), remains a priest continually.
Bashi da uwa bashi da uba, ba shi da lissafin asalin zuriya, ba shi da farkon rayuwa ba shi da karshen rai. Shi firist ne na har abada, kamar Dan Allah.
4 Now consider how great this man was, to whom even Avraham, the patriarch, gave a tenth out of the most valuable plunder.
Yanzu fa dubi irin girman wannan mutum. Kakan kakanninmu Ibrahim ya bada ushira ta abubuwan da ya samo na ganimar yaki gare shi.
5 They indeed of the sons of Lewi who receive the priest's office have a commandment to take tithes of the people according to the Law, that is, of their brothers, though these have come out of the body of Avraham,
Kuma hakika, zuriyar Lawi da suka karbi aikin nan na firistanci suna da umarni daga shari'ar Allah cewa su karbi zakka a gun jama'a, wato, daga yan'uwan su Isra'ilawa, koda shike suma zuriyar Ibrahim ne.
6 but he whose genealogy is not counted from them has accepted tithes from Avraham, and has blessed him who has the promises.
Amma Malkisadak, shi da ba zuriyar Lawi ba ne, ya karbi zakka daga Ibrahim, ya kuma albarkace shi, shi wanda ya ke da alkawarai.
7 But without any dispute the lesser is blessed by the greater.
Ba jayayya, karami shi ke karban albarka daga babba wanda ya girme shi.
8 Here people who die receive tithes, but there one receives tithes of whom it is testified that he lives.
A wannan tsarin mutanen da ke karban zakka wata rana sai ka ga sun mutu, amma a wani kauli mutumin da ya karbi zakka a wurin Ibrahim, ance, wanzaje ne har yau.
9 We can say that through Avraham even Lewi, who receives tithes, has paid tithes,
Kuma bisa ka'ida Lawi, wanda ke karban zakka, shi ma ya bada zakka ga Ibrahim,
10 for he was yet in the body of his father when Malki-Zedeq met him.
Saboda kuwa Lawi na cikin tsatson Ibrahim lokacin da Malkisadak ya gamu da Ibrahim.
11 Now if there was perfection through the Levitical priesthood (for under it the people have received the law), what further need was there for another priest to arise after the order of Malki-Zedeq, and not be called after the order of Ahrun?
Yanzu in da mai yiwuwa ne a sami kammala cikin aikin firistanci na Lawiyawa (domin ta wurin ta ne aka bada shari'a), to ina amfanin wani firist ya zo bisa ga ka'ida irin ta Malkisadak, ba'a kuma ambaci ka'idar Haruna ba?
12 For the priesthood being changed, there is of necessity a change made also in the law.
Don kuwa lokacin da aka canza firistanci, shari'a kuma dole ne a sauya ta.
13 For he of whom these things are said belongs to another tribe, from which no one has officiated at the altar.
Domin mutumin da aka fadi wadannan abubuwa a kansa na wata kabila ne, wadda ba wani mutumin da ya taba yin aiki a kan bagadi.
14 For it is evident that our Lord has sprung out of Yehudah, about which tribe Mushe spoke nothing concerning priests.
Wannan a bayyane yake Ubangijinmu ya zo ne daga zuriyar Yahuza, kabilar da Musa bai taba anbatonsu game da zancen firistanci ba.
15 This is yet more abundantly evident, if after the likeness of Malki-Zedeq there arises another priest,
Abinda muke fadi a bayyane yake cewa, idan wani firist ya taso da kamanin Malkisadak.
16 who has been made, not after the law of a fleshly commandment, but after the power of an endless life:
Wannan sabon firist, ba firist ne da ya taso bisa ga ka'idar zuriya ta yan'adam ba, amma ya zama firist ne ta rayuwa mai iko marar shudewa.
17 for it is testified, "You are a priest forever, according to the order of Malki-Zedeq." (aiōn g165)
Domin a rubuce yake cikin littafi ga me da shi; “Kai firist ne na har'abada bisa ga tsari irin na Malkisadak.” (aiōn g165)
18 For there is an annulling of a foregoing commandment because of its weakness and uselessness
Domin doka ta fari an ajiye ta a gefe guda saboda rarrauna ce kuma marar amfani.
19 (for the law made nothing perfect), and a bringing in of a better hope, through which we draw near to God.
Don kuwa shari'a ba ta iya kamalta kome. Amma fa a kwai bege mai kyau a nan gaba wanda ta gare shi ne zamu sami iso a gun Allah.
20 Inasmuch as he was not made priest without the taking of an oath,
Kuma wannan kyakkyawan bege baya faruwa ba tare da rantsuwa ba, don kuwa su wadancan firistocin ba su dauki wata rantsuwa ba.
21 for they indeed have been made priests without an oath, but he with an oath by him that says of him, "The Lord swore and will not change his mind, 'You are a priest forever, according to the order of Melchizedek.'" (aiōn g165)
Amma Allah yayi rantsuwa game da Yesu cewa, “Ubangiji ya rantse ba kuwa zai fasa tunaninsa ba; 'Kai firist ne har'abada.'” (aiōn g165)
22 Accordingly Yeshua has become the guarantor of a better covenant.
Ta wurin haka Yesu ya bada tabbatacce da kuma ingataccen alkwari.
23 Many, indeed, have been made priests, because they are hindered from continuing by death.
Hakika, mutuwa ta hana firistoci su yi aiki har'abada. Wannan shi ya sa akwai firistoci da yawa daya bayan daya.
24 But he, because he lives forever, has his priesthood unchangeable. (aiōn g165)
Amma da shi ke Yesu na rayuwa ne har'abada, aikinsa na firist ba a musanya shi sam sam. (aiōn g165)
25 Therefore he is also able to save completely those who draw near to God through him, seeing that he lives forever to make intercession for them.
Domin haka kuma yana da cikakken ikon ceton wadanda ke gusowa ga Allah ta wurinsa, domin kullum a raye ya ke yana kuma roko dominsu
26 For such a high priest was indeed fitting for us: holy, guiltless, undefiled, separated from sinners, and made higher than the heavens;
. Domin irin wannan babban firist shi ne ya dace da mu. Ba shi da zunubi, marar abin zargi, tsarkakakke, kebabbe daga masu zunubi, ya na sama da sammai dukka.
27 who does not need, like those high priests, to offer up sacrifices daily, first for his own sins, and then for those of the people. For he did this once for all, when he offered up himself.
Ba shi da bukata, kamar manyan firistoci, da ke mika hadayu kullum, da farko don zunubin kansu, sa'annan don zunubin jama'a dukka. Amma Yesu yayi wannan sau daya tak ba kari don kowa da kowa, yayin da ya mika kansa.
28 For the Law appoints men as high priests who have weakness, but the word of the oath which came after the Law appoints a Son forever who has been perfected. (aiōn g165)
Domin shari'a na nada mutane da ke da gazawa a matsayin firistoci, amma maganar rantsuwa, wadda ta zo a bayan shari'a, ta nada Dan, wanda ya ke cikakke har'abada. (aiōn g165)

< Hebrews 7 >