< Genesis 30 >

1 When Rachel saw that she was not bearing Jacob any children, Rachel envied her sister. She said to Jacob, "Give me children, or else I will die."
Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
2 Then Jacob became very angry with Rachel, and he said, "Am I in God's place, who has withheld from you the fruit of the womb?"
Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
3 She said, "Look, my servant Bilhah. Sleep with her, so that she will bear children for me, that I too may have children through her."
Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
4 So she gave him Bilhah her servant as a wife, and Jacob slept with her.
Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
5 Bilhah conceived, and bore Jacob a son.
ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
6 Rachel said, "God has judged me, and has also heard my voice, and has given me a son." Therefore she called his name Dan.
Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
7 Bilhah, Rachel's handmaid, conceived again, and bore Jacob a second son.
Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
8 Rachel said, "I have wrestled mightily with my sister, and have prevailed." So she named him Naphtali.
Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
9 When Leah saw that she had stopped bearing, she took Zilpah, her servant, and gave her to Jacob as a wife.
Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
10 Zilpah, Leah's handmaid, bore Jacob a son.
Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
11 Leah said, "How fortunate." So she named him Gad.
Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
12 Zilpah, Leah's servant, bore Jacob a second son.
Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
13 Leah said, "Happy am I, for the daughters will call me happy." So she named him Asher.
Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
14 Reuben went out during the wheat harvest and found mandrakes in the field, and brought them to his mother, Leah. Then Rachel said to Leah, "Please give me some of your son's mandrakes."
A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
15 She said to her, "Is it a small matter that you have taken away my husband? Would you take away my son's mandrakes, also?" Rachel said, "Therefore he may sleep with you tonight for your son's mandrakes."
Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
16 Jacob came from the field in the evening, and Leah went out to meet him, and said, "You must sleep with me; for I have surely hired you with my son's mandrakes." So he slept with her that night.
Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
17 God listened to Leah, and she conceived, and bore Jacob a fifth son.
Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
18 Leah said, "God has given me my wages, because I gave my servant to my husband." So she named him Issachar.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
19 Leah conceived again, and bore a sixth son to Jacob.
Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
20 Leah said, "God has given me with a good gift. Now my husband will live with me, because I have borne him six sons." So she named him Zebulun.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
21 Afterwards, she bore a daughter, and named her Dinah.
Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
22 God remembered Rachel, and God listened to her, and made her fertile.
Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
23 She conceived, bore a son, and said, "God has taken away my shame."
Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
24 So she named him Joseph, saying, "May God add another son to me."
Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
25 It happened, when Rachel had borne Joseph, that Jacob said to Laban, "Send me away, that I may go to my own place, and to my country.
Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
26 Give me my wives and my children for whom I have served you, and let me go; for you know the service I have given you."
Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
27 Laban said to him, "If now I have found favor in your eyes, stay here, for I have learned by divination that God has blessed me for your sake."
Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
28 He said, "Name your wages, and I will pay it."
Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
29 He said to him, "You know how I have served you, and how well your livestock have done with me.
Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
30 For you had little before I came, and it has increased abundantly. And the LORD has blessed you wherever I worked. Now when will I also provide for my own household?"
Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
31 He said, "What should I give you?" Jacob said, "You do not need to give me anything. If you will do this one thing for me, I will again pasture your flock and take care of it.
Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
32 I will pass through all your flock today, removing from there every speckled and spotted one, and every black one among the sheep, and the spotted and speckled among the goats. This will be my wages.
Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
33 So my honesty will testify for me later on, when the subject of my wages comes before you. Every one that is not speckled and spotted among the goats, and black among the sheep that I have in my possession, will be counted as stolen."
Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
34 Laban said, "Look, let it be as you have said."
Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
35 That day, he removed the male goats that were streaked and spotted, and all the female goats that were speckled and spotted, every one that had white in it, and all the black ones among the sheep, and put them in the care of his sons.
A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
36 He set three days' journey between himself and Jacob, and Jacob pastured the rest of Laban's flocks.
Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
37 Jacob took fresh branches from poplar, almond and plane trees and made white streaks by peeling them, exposing white stripes on the branches.
Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
38 He set up the peeled branches which he had peeled opposite the flocks in the troughs, that is, the watering places where the flocks came to drink. And since they bred when they came to drink,
Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
39 the flocks bred in front of the branches, and the flocks brought bore streaked, speckled, and spotted.
sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
40 Jacob separated the lambs, and made the flocks face toward the streaked and all the black in the flock of Laban. So he kept his own flocks separate, and did not put them into Laban's flock.
Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
41 It happened, whenever the stronger of the flock were breeding, that Jacob would set up the branches in front of the flock in the troughs, so that they would breed near the branches;
A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
42 but for the weaker of the flock, he did not put them there. So the weaker would be Laban's, and the stronger Jacob's.
amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
43 Thus the man became very rich, and had large flocks, female servants and male servants, and camels and donkeys.
Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.

< Genesis 30 >