< Ezekiel 25 >

1 The word of the LORD came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Son of man, set your face toward the people of Ammon, and prophesy against them:
“Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
3 and tell the people of Ammon, 'Hear the word of the LORD: Thus says the LORD, "Because you said, 'Aha,' against my sanctuary, when it was profaned; and against the land of Israel, when it was made desolate; and against the house of Judah, when they went into captivity:
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
4 therefore, look, I will deliver you to the people of the east for a possession, and they shall set their encampments in you, and make their dwellings in you; they shall eat your fruit, and they shall drink your milk.
saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
5 I will make Rabbah a stable for camels, and the people of Ammon a resting place for flocks: and you shall know that I am the LORD."
Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
6 For thus says the LORD: "Because you have clapped your hands, and stamped with the feet, and rejoiced with all the despite of your soul against the land of Israel;
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
7 therefore, look, I have stretched out my hand on you, and will deliver you for a spoil to the nations; and I will cut you off from the peoples, and I will cause you to perish out of the countries: I will destroy you; and you shall know that I am the LORD."'"
saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
8 "Thus says the LORD: 'Because Moab and Seir say, "Look, the house of Judah is like all the nations";
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
9 therefore, look, I will open the side of Moab from the cities, from his cities which are on his frontiers, the glory of the country, Beth Jeshimoth, Baal Meon, and Kiriathaim,
saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
10 to the people of the east, to go against the people of Ammon; and I will give them for a possession, that the people of Ammon may not be remembered among the nations.
Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
11 and I will execute judgments on Moab; and they shall know that I am the LORD.'"
zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
12 "Thus says the LORD: 'Because Edom has dealt against the house of Judah by taking vengeance, and has greatly offended, and revenged himself on them';
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
13 therefore thus says the LORD, 'I will stretch out my hand on Edom, and will cut off man and animal from it; and I will make it desolate from Teman; even to Dedan shall they fall by the sword.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
14 I will lay my vengeance on Edom by the hand of my people Israel; and they shall do in Edom according to my anger and according to my wrath; and they shall know my vengeance, says the LORD.'"
Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 "Thus says the LORD: 'Because the Philistines have dealt by revenge, and have taken vengeance with despite of soul to destroy with perpetual enmity;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
16 therefore thus says the LORD, Look, I will stretch out my hand on the Philistines, and I will cut off the Cherethites, and destroy the remnant of the sea coast.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
17 I will execute great vengeance on them with wrathful rebukes; and they shall know that I am the LORD, when I shall lay my vengeance on them.'"
Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”

< Ezekiel 25 >