< 2 Timothy 4 >

1 I command you therefore before God and Meshikha Yeshua, who will judge the living and the dead, and by his appearing and his Kingdom:
Ina bada wannan umarni a gaban Allah da Yesu Almasihu, wanda zai yi wa rayayyu da matattu shari'a, kuma saboda bayyanuwarsa da mulkinsa:
2 preach the word; be urgent in season and out of season; reprove, rebuke, and exhort, with all patience and teaching.
Ka yi wa'azin Kalma. Ka himmantu a kai ko da zarafi ko ba zarafi. Ka tsautar, ka kwabar, ka gargadar, da dukan hakuri da koyarwa.
3 For the time will come when they will not listen to the sound doctrine, but, having itching ears, will heap up for themselves teachers after their own lusts;
Gama lokaci na zuwa wanda mutane ba za su jure wa koyarwar kirki ba. Maimakon haka, zasu tattara wa kansu malamai bisa ga sha'awowin zuciyarsu. Za su rika fada masu abin da kunnuwansu ke so.
4 and will turn away their ears from the truth, and turn aside to myths.
Za su juya kunnuwansu daga koyarwar gaskiya, za su koma wa tatsunniyoyi na banza.
5 But you be sober in all things, endure hardship, do the work of an evangelist, fulfill your ministry.
Amma kai, sai ka natsu a cikin dukan abubuwa. Ka jure wa wahala; ka yi aikin mai bishara, ka cika hidimarka.
6 For I am already being offered, and the time of my departure has come.
Gama ana-tsiyaye ni. Lokacin yin kaurata yayi.
7 I have fought the good fight. I have finished the course. I have kept the faith.
Na yi tsere na gaskiya; na kuma kammala tseren; na rike bangaskiya.
8 From now on, there is stored up for me the crown of righteousness, which the Lord, the righteous judge, will give to me on that day; and not to me only, but also to all those who have loved his appearing.
An adana mani rawani na adalci, wanda Ubangiji, alkali mai adalci, zai ba ni a ranan nan. Ba ni kadai ba, amma kuma ga dukkan wadanda suke kaunar zuwansa.
9 Be diligent to come to me soon,
Ka yi iyakacin kokarinka ka zo wurina da sauri.
10 for Demas left me, having loved this present world, and went to Thessalonica; Crescens to Galatia, and Titus to Dalmatia. (aiōn g165)
Domin Dimas ya yashe ni. Ya kaunaci wannan duniyar, ya tafi Tassalonika, Kariskis ya tafi Galatiya, Titus kuma ya tafi Dalmatiya. (aiōn g165)
11 Only Luqa is with me. Take Markos, and bring him with you, for he is useful to me for service.
Luka ne kadai yake tare da ni. Ka nemo Markus ka zo tare da shi domin yana da amfani a gareni a cikin aikin.
12 But I sent Tychicus to Ephesus.
Na aiki Tikikus zuwa Afisus.
13 Bring the cloak that I left at Troas with Carpus when you come, and the books, especially the parchments.
Ka kawo mani mayafin da na bari a Taruwasa wurin Karbus, idan za ka zo ka taho da shi, duk da littatafan nan, musanman takardun nan.
14 Alexandros, the coppersmith, did much evil to me. The Lord will repay him according to his works,
Iskandari makerin dalma ya kulla mani makirci ba kadan ba. Ubangiji zai biya shi gwargwadon ayyukansa.
15 of whom you also must beware; for he greatly opposed our words.
Kai ma ka yi hankali da shi, domin yana tsayyaya da maganganunmu sosai.
16 At my first defense, no one came to help me, but all left me. May it not be held against them.
Da farkon kariyar kaina, babu wanda ya goyi bayana. Maimakon haka kowa ya guje ni. Bana so dai a lissafta wannan a kansu.
17 But the Lord stood by me, and strengthened me, that through me the message might be fully proclaimed, and that all the non-Jewish people might hear; and I was delivered out of the mouth of the lion.
Amma Ubangiji ya kasance tare da ni, ya kuma karfafa ni, yadda ta wurina, shelar ta sami cika da kyau, domin dukan al'ummai su ji. An kwato ni daga bakin zaki.
18 And the Lord will deliver me from every evil work, and will preserve me for his heavenly Kingdom; to whom be the glory forever and ever. Amen. (aiōn g165)
Allah zai kubutar ni daga dukan ayyukan mugunta, ya kuma cece ni domin mulkinsa na sama. Daukaka ta tabatta a gareshi har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
19 Greet Prisca and Aquila, and the house of Onesiphorus.
Ka gayar da Briskilla, da Akila, da gidan Onisifurus.
20 Erastus remained at Corinth, and I left Trophimus at Miletus, ill.
Arastus ya nan zaune a Korinti, amma na bar Turufimus ya na zazzabi a Militus.
21 Be diligent to come before winter. Eubulus salutes you, as do Pudens, Linus, Claudia, and all the brothers.
Ka yi iyakar kokarinka, ka zo kamin hunturu. Yubulus yana gayar da kai, haka ma Budis da Linus da Kalafidiya da dukan 'yan'uwa.
22 The Lord be with your spirit. Grace be with you.
Bari Ubangiji ya kasance tare da ruhunka. Bari Alheri ya kasance da kai.

< 2 Timothy 4 >