< 2 Corinthians 5 >

1 For we know that if the earthly house of our tent is dissolved, we have a building from God, a house not made with hands, everlasting, in the heavens. (aiōnios g166)
Mun san cewa idan wannan gidan da muke zaune a ciki ya rushe, muna da wani ginin daga wurin Allah. Gida ne wanda ba hannuwan mutane suka gina ba, amma madawwamin gida ne a cikin sama. (aiōnios g166)
2 For truly in this we groan, longing to be clothed with our habitation which is from heaven,
Domin a cikin wannan jiki muna gurnani, muna jira a suturta mu da wurin zaman mu na samaniya.
3 since, after we have put it on, we will not be found naked.
Muna jiran wannan ne domin ta wurin suturtar da mu ba za a same mu tsirara ba.
4 For indeed we who are in this tent do groan, being burdened; not that we desire to be unclothed, but that we desire to be clothed, that what is mortal may be swallowed up by life.
Gama babu shakka yayinda muke cikin wannan alfarwa, muna gurnani, muna nawaita. Ba mu so muyi zaman hutanci. Maimakon haka, muna so a suturtar da mu, domin rai ya hadiye abu mai mutuwa.
5 Now he who made us for this very thing is God, who also gave to us the down payment of the Rukha.
Wanda kuwa yake shirya mu domin ainihin wannan abu Allah ne, wanda ya ba mu Ruhu a matsayin alkawarin abinda ke zuwa.
6 Therefore, we are always confident and know that while we are at home in the body, we are absent from the Lord;
Domin wannan mu zama da gabagadi koyaushe. Mu lura da cewa yayinda muka shagala cikin jiki, muna nesa da Ubangiji.
7 for we walk by faith, not by sight.
Gama bisa ga bangaskiya muke tafiya, ba bisa ga ganin ido ba.
8 We are of good courage, I say, and are willing rather to be absent from the body, and to be at home with the Lord.
Don haka muna da gabagadi. Mun gwammace mu rabu da jiki domin mu zauna tare da Ubangiji.
9 Therefore also we make it our aim, whether at home or absent, to be well pleasing to him.
Sai muka maishe shi burinmu, ko muna cikin jiki ko nesa, mu gamshe shi.
10 For we must all appear before the judgment seat of Meshikha; that each one may receive the things in the body, according to what he has done, whether good or bad.
Domin tilas dukanmu mu hallara a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, saboda kowa ya karbi sakamakon abubuwan da yayi cikin jiki, ko masu kyau ne ko marasa kyau.
11 Knowing therefore the fear of the Lord, we persuade people, but we are revealed to God; and I hope that we are revealed also in your consciences.
Don haka, domin mun san tsoron Ubangiji, muna rinjayar mutane. Allah na ganin yadda muke a fili. Ina fatan hakan a fili take ga lamirinku.
12 We are not commending ourselves to you again, but speak as giving you occasion of boasting on our behalf, that you may have something to answer those who boast in appearance, and not in heart.
Ba muna kokarin mu rinjaye ku domin ku kalle mu a matsayin amintattun mutane ba. Maimakon haka, muna ba ku dalilin yin takama da mu, domin ku sami amsar da za ku bada ga wadanda ke fahariya da kasancewarsu amma ba game da abinda ke zuciya ba.
13 For if we are out of control, it is for God. If we are in a reasonable way, it is for you.
Gama idan mun fita daga hankulanmu, saboda Allah ne. Kuma idan muna cikin hankalinmu, domin ku ne.
14 For the love of Meshikha constrains us; because we judge thus, that one died for all, therefore all died.
Domin kaunar Almasihu ta tilas ta mu, domin mun tabbatar da wannan: cewa mutum daya ya mutu domin kowa, kuma domin wannan duka sun mutu.
15 He died for all, that those who live should no longer live to themselves, but to him who for their sakes died and rose again.
Kuma Almasihu ya mutu domin kowa, domin wadanda ke raye kada su sake rayuwa domin kansu. A maimakon haka, su yi rayuwa domin shi wanda ya mutu kuma aka tashe shi.
16 Therefore we know no one after the flesh from now on. Even though we have known Meshikha after the flesh, yet now we no longer know him in this way.
Domin wannan dalili, daga yanzu ba za mu kara shar'anta kowa bisa ga ma'aunin 'yan'adam ba, ko da yake a baya mun taba duban Almasihu a haka. Amma yanzu mun daina shar'anta kowa ta haka.
17 Therefore if anyone is in Meshikha, he is a new creation. The old things have passed away. Look, new things have come.
Saboda haka, duk wanda ke cikin Almasihu, sabon halitta ne. Tsofaffin al'amura sun shude. Duba, sun zama sababbi.
18 But all things are of God, who reconciled us to himself through Yeshua Meshikha, and gave to us the ministry of reconciliation;
Dukan wadannan abubuwa daga Allah ne. Ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu hidimar sulhu.
19 namely, that God was in Meshikha reconciling the world to himself, not counting their trespasses against them, and having committed to us the word of reconciliation.
Wato, cikin Almasihu, Allah na sulhunta duniya zuwa gare shi, ba tare da lissafin zunubansu a kansu ba. Yana damka mana sakon sulhu.
20 We are therefore ambassadors on behalf of Meshikha, as though God were making his appeal through us. We implore you on behalf of Meshikha, be reconciled to God.
Don haka an zabe mu a matsayin wakilan Almasihu, kamar dai Allah na kira ga mutane ta wurin mu. Muna rokon ku, saboda Almasihu: ''ku sulhuntu ga Allah!''
21 For him who knew no sin he made to be sin on our behalf; so that in him we might become the righteousness of God.
Shi ya maida Almasihu ya zama hadaya domin zunubinmu. Shine wanda bai taba zunubi ba. Ya yi haka ne don mu zama adalchin Allah a cikin sa.

< 2 Corinthians 5 >