< 1 Samuel 31 >

1 Now the Philistines fought against Israel: and the men of Israel fled from before the Philistines, and fell down slain on Mount Gilboa.
Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa, sai Isra’ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka kuma karkashe da yawa a dutsen Gilbowa.
2 The Philistines followed hard on Saul and on his sons; and the Philistines killed Jonathan, and Abinadab, and Malkishua, the sons of Saul.
Filistiyawa suka abka wa Shawulu da’ya’yansa maza, suka kashe’ya’yan Shawulu. Yonatan da Abinadab da Malki-Shuwa.
3 The battle was fierce against Saul, and the archers found him, and he was wounded by the archers.
Yaƙin ya yi zafi ƙwarai kewaye da Shawulu, har maharba suka ji masa ciwo sosai bayan sun sha ƙarfinsa.
4 Then Saul said to his armor bearer, "Draw your sword, and thrust me through with it, lest these uncircumcised come and thrust me through, and torture me." But his armor bearer would not; for he was terrified. Therefore Saul took his sword, and fell on it.
Sai Shawulu ya ce wa mai ɗauka masa makami, “Ka zare takobinka ka soke ni, kada waɗannan marasa kaciya su zo su ci mini mutunci, su kashe ni.” Amma mai ɗaukan makaman bai yarda ba don ya ji tsoro sosai. Sai Shawulu ya zāre takobinsa ya soki kansa.
5 When his armor bearer saw that Saul was dead, he likewise fell on his sword, and died with him.
Da mai ɗaukar makamai ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya zāre takobinsa ya soki kansa ya mutu.
6 So Saul died, and his three sons, and his armor bearer, and all his men, that same day together.
Shawulu da yaransa uku da mai ɗaukar makamansa da dukan mutanensa suka mutu a rana ɗaya.
7 When the men of Israel who were on the other side of the valley, and those who were beyond the Jordan, saw that the men of Israel fled, and that Saul and his sons were dead, they abandoned their cities, and fled; and the Philistines came and lived in them.
Sa’ad da Isra’ilawa na bakin kwari da waɗanda suke hayin Urdun suka ga sojojin Isra’ila suna gudu, Shawulu da yaransa uku kuma duk sun mutu, sai suka bar mallakansu suka sheƙa da gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka mamaye wuraren.
8 It happened on the next day, when the Philistines came to strip the slain, that they found Saul and his three sons fallen on Mount Gilboa.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo domin su washe kayan matattun, sai suka tarar Shawulu da’ya’yansa uku duk sun mutu, a dutsen Gilbowa.
9 They cut off his head, and stripped off his armor, and sent into the land of the Philistines all around, to carry the news to their idols, and to the people.
Suka sare kansa suka tuɓe makamansa, suka aika manzanni a dukan ƙasar Filistiyawa, su ba da labarin a haikalin allolinsu da cikin mutanensu.
10 They put his armor in the house of the Ashtaroth; and they fastened his body to the wall of Beth Shan.
Suka ajiye makaman Shawulu a cikin haikalin gumakan Ashtarot. Suka kafa gawarsa a kan katanga Bet-Shan.
11 But when the inhabitants of Jabesh Gilead heard what the Philistines had done to Saul,
Sa’ad da mutanen Yabesh Gileyad suka sami labarin abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu.
12 all the valiant men arose and traveled all night, and took the body of Saul and the bodies of his sons from the wall of Beth Shan, and brought them to Jabesh and burnt them there.
Sai dukan jarumawansu suka tashi cikin dare suka tafi Bet-Shan suka saukar da gawar Shawulu da na’ya’yansa daga kan katangan Bet-Shan suka tafi Yabesh inda suka ƙone su.
13 They took their bones, and buried them under the tamarisk tree in Jabesh, and fasted seven days.
Sai suka kwashi ƙasusuwansu suka binne a gindin itace tsamiya a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.

< 1 Samuel 31 >