< 1 John 3 >

1 Look at how great a love the Father has bestowed on us, that we should be called children of God; and such we are. For this cause the world does not know us, because it did not know him.
Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba.
2 Beloved, now we are children of God, and it is not yet revealed what we will be. We know that, when he is revealed, we will be like him; for we will see him just as he is.
Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake.
3 Everyone who has this hope set on him purifies himself, even as he is pure.
Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.
4 Everyone who sins also commits lawlessness. Sin is lawlessness.
Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne.
5 You know that he was revealed to take away sins, and in him is no sin.
Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi.
6 Whoever remains in him does not sin. Whoever sins hasn't seen him, neither knows him.
Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.
7 Children, let no one lead you astray. He who does righteousness is righteous, even as he is righteous.
'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali.
8 He who sins is of the devil, for the devil has been sinning from the beginning. To this end the Son of God was revealed, to destroy the works of the devil.
Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.
9 Whoever is born of God does not commit sin, because his seed remains in him; and he cannot sin, because he is born of God.
Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah.
10 In this the children of God are revealed, and the children of the devil. Whoever does not do righteousness is not of God, neither is he who does not love his brother.
Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.
11 For this is the message which you heard from the beginning, that we should love one another;
Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu,
12 unlike Qayen, who was of the evil one, and killed his brother. Why did he kill him? Because his works were evil, and his brother's righteous.
ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.
13 Therefore do not be surprised, brothers, if the world hates you.
Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku.
14 We know that we have passed out of death into life, because we love the brothers. He who does not love remains in death.
Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne.
15 Whoever hates his brother is a murderer, and you know that no murderer has everlasting life remaining in him. (aiōnios g166)
Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai. (aiōnios g166)
16 By this we know love, because he laid down his life for us. And we ought to lay down our lives for the brothers.
Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu.
17 But whoever has the world's goods, and sees his brother in need, and closes his heart of compassion against him, how does the love of God remain in him?
Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa?
18 Little children, let us not love in word only, neither with the tongue only, but in deed and truth.
'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.
19 And by this we will know that we are of the truth, and persuade our heart before him,
Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa.
20 because if our heart condemns us, God is greater than our heart, and knows all things.
Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome.
21 Beloved, if our hearts do not condemn us, we have confidence before God;
Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah.
22 and whatever we ask, we receive from him, because we keep his commandments and do the things that are pleasing in his sight.
Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.
23 This is his commandment, that we should believe in the name of his Son, Yeshua Meshikha, and love one another, even as he commanded us.
Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka.
24 He who keeps his commandments remains in him, and he in him. By this we know that he remains in us, by the Rukha which he gave us.
Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.

< 1 John 3 >