< Luke 8 >

1 It happened shortly afterwards that he began to go from town to town and village to village, preaching and telling the good news of the kingdom of God.
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 The twelve were with him, and certain women whom he had delivered from evil spirits and various diseases. Mary of Magdala, out of whom seven demons have been driven,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 and Joanna, the wife of Chuza, Herod’s steward, and Susanna, and many other women, who used to minister to him out of their substance.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 As a great crowd was gathering, and men of town after town kept restoring to him, he spoke a parable to them.
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 "A sower went out to sow his seed, and as he sowed some fell by the wayside, and was trodden under foot, and the wild birds ate it up.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 "Some other seed dropped on the rock, as soon as it grew it withered away, because it had no moisture.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 "Another part fell among the thorns; and the thorns grew with it and choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 "But some fell on good soil, and grew up, and brought forth fruit, a hundredfold." When he said this, he called out, "Whoever has ears to hear with, let him listen."
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Then his disciples began to interrupt him, saying, "What does this parable mean?"
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 He answered. "To you it is given to understand the mysteries of the kingdom of God; But all others are taught in parables so that seeing they shall not see, and hearing they shall not hear.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 "This is the meaning of the parable. The seed is the word of God.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 "Those by the wayside are people who hear, but then comes the devil and carries off the word from their heart, so that they may not believe and not be saved.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 "Those on the rock are people who, upon hearing, receive the word with joy; but they have no root. For a time indeed they all believe, but in time of temptation they fall away.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 "And that which fell upon thorns is those who have heard, but as they go on their way of word is choked with the cares and riches and pleasures of life; so they bring no fruit of perfection.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 "And that in the good soil is those who have listened to the message and, in an honest and good heart, hold fast, and bring forth fruit with patience.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 "When he lights a lamp no one covers it with a vase or hides it under a bed; he puts it on a lamp-stand so whoever may behold the light.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 "For is nothing hidden that shall not be disclosed; there is nothing secret which shall not be made known and come to the light.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 "Take heed, then, how you listen. for he who has, to him shall it be given, but from him who has not, shall be taken away even what he has."
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 There came to him his mother and his brothers, and they could not reach him because of the crowd.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 But some one told him, "Your mother and brothers are standing outside, desiring to see you."
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 "My mother and brothers," he answered, "are those who listen to the word of God and obey it."
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Now it happened that one of these days he got into a boat, And him his disciples, and he said to them, "Let us cross to the other side of the lake."
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 So they set sail. While they were sailing he fell asleep. And there fell on the lake a squall of wind, so that the boat began to fill, and they to be in deadly peril.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Then they came to him and woke him, saying, "Master, Master, we are lost!" Then he awoke, and rebuked the winds and the raging of the sea. They ceased, and there was a calm.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 "Where is your faith?" he asked them, In their terror they were filled with amazement, and said to one another, "Who is this who commands even the winds and the sea, and they obey him?"
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Then they put in at the country of Gadarenes, which is across from Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 When he landed here he was met by a certain townsman who was possessed by demons. For a long time he had worn no clothes and nor lived in any house, but in tombs.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 When he saw Jesus he cried out, and fell down before him, and in a loud voice exclaimed. "What have we to do with you, Jesus, you son of God Most High? I implore you to torment me not!"
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 For Jesus was already commanding the unclean spirit to come out of the man. For many times it had seized him and held him, and they again and again kept him under guard, and put him in chains and fetters. But he would break his bonds asunder, as he was driven by the demon in to the desert.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 So Jesus asked him, "What is your name?" And he answered, "Legion" (for many demons had entered into him).
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 So they besought Jesus not to command them to go away into the abyss. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Now there was a great herd of swine feeding on the hillside, and the demons begged him to give them leave to enter them. He gave them leave.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 The demons came out of the man, and entered into the swine; the herd rushed violently down over the cliff into the lake.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 And those who saw what had happened fled and reported it in the town and the villages.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Then the people came out to see what had happened, and came to Jesus, and found the man out of whom the demons had gone sitting clothed and in his right mind, at the feet of Jesus. And they were terrified.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Then those who had seen it told them how the demon-possessed man had been saved.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 And the whole populace of Gadarenes and the surrounding territory besought Jesus to go away from them; for they were terror-stricken. So he entered a boat and returned.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 But the man out of whom the demons had gone kept begging him that he might be with him. But Jesus sent him away saying,
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 "Return to your home, and tell them all that God has done for you." So he went away and throughout the whole city he published how much Jesus had done for him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 And as Jesus returned the crowd welcomed him;
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 for they were all waiting for him. Just then there came a man named Jarius, and he was ruler in the synagogue. He fell down at Jesus’ feet and begged him to come into his house;
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 for he had only one daughter, about twelve years of age, and she lay dying. But as he went the crowds continued to press in on him.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 And a woman who for twelve years had had a hemorrhage, and had spent on doctors all that she had, but none had cured her,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 came close behind him, and touched the hem of his garment; and instantly the hemorrhage ceased.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 "Who is that touched me?" said Jesus and when everybody denied it, Peter said, "Master, the crowds are hemming you in and pressing upon you."
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 But Jesus said. "Some one did touch me; for I perceived that the power was proceeding out of me."
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Then the woman, who saw that she had not escaped notice, came trembling, and falling down before him, stated before the people for what reason she had touched him, and how she had been instantly healed.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 "Daughter," he said "your faith has made you well, go on into peace."
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 As he was speaking some one came from the house of the synagogue, saying. "Your daughter is dead! Do not trouble the Master."
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 But Jesus heard and answered. "Have no fear. Only believe, and she shall be restored."
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 So he came to the house, and would not permit anyone to go in with him except Peter and Johnand James, and the father and Mother of the little girl.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 The people were weeping and bewailing her, but he said. "Stop your wailing; for she is not dead, but asleep."
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 They began to laugh him to scorn, because they knew well that she was dead.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 But he took her by the hand and called to her, "Little daughter, rise!"
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 And her spirit returned and instantly she stood up.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 He bade them to get her some food. Her parents were amazed; but he forbade them to tell any one what had been done.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >