< Luke 1 >

1 Seeing that many took in hand to set in order a narration of the matters that have been fully assured among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 as they delivered to us, who from the beginning became eyewitnesses, and officers of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good also to me, having followed from the first after all things exactly, to write to you in order, most noble Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that you may know the certainty of the things wherein you were instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, the king of Judea, a certain priest, by name Zacharias, of the division of Abijah, and his wife of the daughters of Aaron, and her name Elizabeth;
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 and they were both righteous before God, going on in all the commands and righteousnesses of the LORD blameless,
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 and they had no child, because that Elizabeth was barren, and both were advanced in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, in his acting as priest, in the order of his division before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood, his lot was to make incense, having gone into the temple of the LORD,
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and all the multitude of the people were praying outside, at the hour of the incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him a messenger of the LORD standing on the right side of the altar of the incense,
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 and Zacharias, having seen, was troubled, and fear fell on him;
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 and the messenger said to him, “Do not fear, Zacharias, for your supplication was heard, and your wife Elizabeth will bear a son to you, and you will call his name John,
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 and there will be joy to you, and gladness, and many will rejoice at his birth,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 for he will be great before the LORD, and wine and strong drink he may not drink, and he will be full of the Holy Spirit, even from his mother’s womb;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 and he will turn many of the sons of Israel to the LORD their God,
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 and he will go before Him, in the spirit and power of Elijah, to turn hearts of fathers to children, and disobedient ones to the wisdom of righteous ones, to make ready for the LORD, a people prepared.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said to the messenger, “Whereby will I know this? For I am aged, and my wife is advanced in her days?”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the messenger answering said to him, “I am Gabriel, who has been standing near before God, and I was sent to speak to you, and to proclaim this good news to you,
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 and behold, you will be silent, and not able to speak, until the day that these things will come to pass, because you did not believe my words that will be fulfilled in their season.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias, and wondering at his lingering in the temple,
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 and having come out, he was not able to speak to them, and they perceived that he had seen a vision in the temple, and he was beckoning to them, and remained mute.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his service were fulfilled, he went away to his house,
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 and after those days, his wife Elizabeth conceived, and hid herself five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “Thus the LORD has done to me, in days in which He looked on [me], to take away my reproach among men.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in the sixth month the messenger Gabriel was sent by God, to a city of Galilee, the name of which [is] Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin, betrothed to a man, whose name [is] Joseph, of the house of David, and the name of the virgin [is] Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the messenger having come in to her, said, “Greetings, favored one, the LORD [is] with you; blessed [are] you among women”;
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 and she, having seen, was troubled at his word, and was reasoning of what kind this salutation may be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the messenger said to her, “Do not fear, Mary, for you have found favor with God;
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 and behold, you will conceive in the womb, and will bring forth a Son, and call His Name Jesus;
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great, and He will be called Son of the Highest, and the LORD God will give Him the throne of His father David,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and He will reign over the house of Jacob for all ages; and of His kingdom there will be no end.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mary said to the messenger, “How will this be, seeing I do not know a husband?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the messenger answering said to her, “The Holy Spirit will come on you, and the power of the Highest will overshadow you, therefore also the holy-begotten thing will be called Son of God;
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 and behold, Elizabeth, your relative, she also has conceived a son in her old age, and this is the sixth month to her who was called barren;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 because nothing will be impossible with God.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said, “Behold, the maidservant of the LORD; let it be to me according to your saying,” and the messenger went away from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary having arisen in those days, went into the hill-country, with haste, to a city of Judea,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zacharias, and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elizabeth heard the salutation of Mary, the baby leapt in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and spoke out with a loud voice and said, “Blessed [are] you among women, and blessed [is] the Fruit of your womb;
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 and from where [is] this to me, that the mother of my Lord might come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For behold, when the voice of your salutation came to my ears, the baby in my womb leapt in gladness;
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 and blessed [is] she who believed, for there will be a completion to the things spoken to her from the LORD.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, “My soul magnifies the LORD,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit was glad on God my Savior,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Because He looked on the lowliness of His maidservant, For behold, from now on all the generations will call me blessed,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For He who is mighty did great things to me, And holy [is] His Name,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And His kindness [is] to generations of generations, To those fearing Him;
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He did powerfully with His arm, He scattered abroad the proud in the thought of their heart,
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He brought down the mighty from thrones, And He exalted the lowly,
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He filled the hungry with good, And the rich He sent away empty;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has taken hold of His servant Israel, To remember kindness,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 As He spoke to our fathers, To Abraham and to his seed—throughout the age.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary remained with her about three months, and turned back to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 And to Elizabeth was the time fulfilled for her bringing forth, and she bore a son,
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 and the neighbors and her relatives heard that the LORD was making His kindness great with her, and they were rejoicing with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, on the eighth day, they came to circumcise the child, and they were calling him by the name of his father, Zacharias,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 and his mother answering said, “No, but he will be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, “There is none among your relatives who is called by this name,”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 and they were making signs to his father, what he would wish him to be called,
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 and having asked for a tablet, he wrote, saying, “John is his name”; and they all wondered;
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 and his mouth was opened immediately, and his tongue, and he was speaking, praising God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came on all those dwelling around them, and in all the hill-country of Judea were all these sayings spoken of,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 and all who heard laid them up in their hearts, saying, “What then will this child be?” And the hand of the LORD was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father Zacharias was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blessed [is] the LORD, the God of Israel, Because He looked on, And worked redemption for His people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And raised a horn of salvation to us, In the house of His servant David,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As He spoke by the mouth of His holy prophets, Which have been from the age; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Salvation from our enemies, And out of the hand of all hating us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To do kindness with our fathers, And to be mindful of His holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 An oath that He swore to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 To give to us, without fear, Having been delivered out of the hand of our enemies,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 To serve Him, in holiness and righteousness Before Him, all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, Prophet of the Highest will you be called; For you will go before the face of the LORD, To prepare His ways.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give knowledge of salvation to His people In forgiveness of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through the yearnings of our God, In which the rising from on high looked on us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To give light to those sitting in darkness and death-shade, To guide our feet to a way of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and was strengthened in spirit, and he was in the deserts until the day of his showing to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >