< 2 Kings 13 >

1 In the three and twentieth year of Joash the son of Achazyahu the king of Judah became Jehoachaz the son of Jehu king over Israel in Samaria [for] seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 And he did what is evil in the eyes of the Lord, and followed the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin: he departed not therefrom.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 And the anger of the Lord was kindled against Israel; and he gave them up into the hand of Chazael the king of Syria, and into the hand of Ben-hadad the son of Chazael, all the time.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 And Jehoachaz besought the Lord; and the Lord hearkened unto him; for he saw the oppression of Israel, how the king of Syria oppressed them.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 (And the Lord gave Israel a deliverer, so that they came out from under the power of the Syrians: and the children of Israel dwelt in their tents, as in times past.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Nevertheless they departed not from the sins of the house of Jerobo'am, who induced Israel to sin, therein the people walked: and the Asherah also remained standing in Samaria.)
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 For he had left of people to Jehoachaz none but fifty horsemen, and ten chariots, and ten thousand men on foot; for the king of Syria had destroyed them, and had made them like the dust at threshing.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Now the rest of the acts of Jehoachaz, and all that he did, and his mighty deeds, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 And Jehoachaz slept with his fathers; and they buried him in Samaria: and Joash his son became king in his stead.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the thirty and seventh year of Joash the king of Judah became Jehoash the son of Jehoachaz king over Israel in Samaria, [for] sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 And he did what is evil in the eyes of the Lord; he departed not from all the sins of Jerobo'am the son of Nebat, who induced Israel to sin: therein he walked.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 And the rest of the acts of Joash, and all that he did, and his mighty deeds wherewith he fought against Amazyah the king of Judah, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 And Joash slept with his fathers; and Jerobo'am sat upon his throne: and Joash was buried in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Now Elisha' was fallen sick of his sickness whereof he had to die. And Joash the king of Israel came down unto him, and wept over his face, and said, O my father, my father, the chariot of Israel, and their horsemen.
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 And Elisha' said unto him, Fetch a bow and arrows. And he fetched unto him a bow and arrows.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 And he said to the king of Israel, Place thy hand upon the bow. And he placed his hand [upon it]: and Elisha' laid his hands upon the king's hands.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 And he said, Open the window eastward. And he opened it. Then said Elisha', Shoot. And he shot. And he said, The arrow of victory from the Lord, and the arrow of victory over Syria; and thou shalt smite the Syrians in Aphek, till they be consumed.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 And he said, Take the arrows. And he took them. And he said unto the king of Israel, Strike upon the ground. And he struck three times, and stopped.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 And the man of God was angry with him, and said, Thou shouldst have struck five or six times; then wouldst thou have smitten the Syrians till they had been consumed: whereas now thou shalt smite the Syrians three times.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 And Elisha' died, and they buried him. And the predatory bands of Moabites frequently invaded the land at the coming in of the year.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 And it came to pass, as they were burying a man, that, behold, they saw the band; and they cast down the man into the sepulchre of Elisha': and as the man came, and touched the bones of Elisha', he revived, and rose up on his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 But Chazael the king of Syria oppressed Israel all the days of Jehoachaz.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 And the Lord became gracious unto them, and had mercy on them, and turned his regard unto them, because of his covenant with Abraham, Isaac, and Jacob, and would not destroy them, and he cast them not off from his presence even until now.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 And Chazael the king of Syria died: and Ben-hadad his son became king in his stead.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 And Jehoash the son of Jehoachaz took again the cities out of the power of Ben-hadad the son of Chazael, which he had taken out of the power of Jehoachaz his father in the war. Three times did Joash beat him, and he recovered the cities of Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >