< Zacharias 5 >

1 And I turned, and lifted up mine eyes, and looked and behold a flying sickle.
Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
2 And he said to me, What see you? And I said, I see a flying sickle, of the length of twenty cubits, and of the breadth of ten cubits.
Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
3 And he said to me, This is the curse that goes forth over the face of the whole earth: for every thief shall be punished with death on this side, and every false swearer shall be punished on that side.
Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
4 And I will bring it forth, says the Lord Almighty, and it shall enter into the house of the thief, and into the house of him that swears falsely by my name: and it shall rest in the midst of his house, and shall consume it, and the timber of it, and the stones of it.
Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
5 And the angel that talked with me went forth, and said to me, Lift up your eyes, and see this that goes forth.
Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
6 And I said, What is it? And he said, This is the measure that goes forth. And he said, This is their iniquity in all the earth.
Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
7 And behold a talent of lead lifted up: and behold a woman sat in the midst of the measure.
Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
8 And he said, This is iniquity. And he cast it into the midst of the measure, and cast the weight of lead on the mouth of it.
Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
9 And I lifted up mine eyes, and saw, and, behold, two women coming forth, and the wind was in their wings; and they had stork's wings: and they lifted up the measure between the earth and the sky.
Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
10 And I said to the angel that spoke with me, Whither do these carry away the measure?
Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
11 And he said to me, To build it a house in the land of Babylon, and to prepare [a place for it]; and they shall set it there on its own base.
Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”

< Zacharias 5 >