< Psalms 77 >

1 For the end, for Idithun, a Psalm of Asaph. I cried to the Lord with my voice, yes, my voice [was addressed] to God; and he gave heed to me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In the day of mine affliction I earnestly sought the Lord; [even] with my hands by night before him, and I was not deceived; my soul refused to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I remembered God, and rejoiced; I poured out my complaint, and my soul fainted. (Pause)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 All mine enemies set a watch [against me]: I was troubled, and spoke not.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I considered the days of old, and remembered ancient years.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 And I meditated; I communed with my heart by night, and diligently searched my spirit, [saying],
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Will the Lord cast off for ever? and will he be well pleased no more?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Will he cut off his mercy for ever, even for ever and ever?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Will God forget to pity? or will he shut up his compassions in his wrath? (Pause)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 And I said, Now I have begun; this is the change of the right hand of the Most High.
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I remembered the works of the Lord; for I will remember your wonders from the beginning.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 And I will meditate on all your works, and will consider your doings.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 O God, your way is in the sanctuary; who is a great God as our God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 You are the God that do wonders; you have made known your power among the nations.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 You have with your arm redeemed your people, the sons of Jacob and Joseph. (Pause)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters saw you, O God, the waters saw you, and feared; and the depths were troubled.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 [There was] an abundant sound of waters: the clouds uttered a voice; for your arrows went abroad.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 The voice of your thunder was abroad, and around your lightnings appeared to the world; the earth trembled a quaked.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Your way is in the sea, and your paths in many waters, and your footsteps can’t be known.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 You did guide your people as sheep by the hand of Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Psalms 77 >