< Psalms 68 >

1 For the end, a Psalm of a Song by David. Let God arise, and let his enemies be scattered; and let them that hate him flee from before him.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 As smoke vanishes, let them vanish: as wax melts before the fire, so let the sinners perish from before God.
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 But let the righteous rejoice; let them exult before God: let them be delighted with joy.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Sing to God, sing praises to his name: make a way for him that rides upon the west (the Lord is his name) and exult before him. They shall be troubled before the face of him,
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 [who is] the father of the orphans, and judge of the widows: [such is] God in his holy place.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 God settles the solitary in a house; leading forth prisoners mightily, also them that act provokingly, [even] them that dwell in tombs.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 O God, when you went forth before your people, when you went through the wilderness; (Pause)
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 the earth quaked, yes, the heavens dropped [water] at the presence of the God of Sina, at the presence of the God of Israel.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 O God, you will grant to your inheritance a gracious rain; for it was weary, but you did refresh it.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Your creatures dwell in it: you have in your goodness prepared for the poor.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 The Lord God will give a word to them that preach [it] in a great company.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 The king of the forces of the beloved, of the beloved, [will] even [grant them] for the beauty of the house to divide the spoils.
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 Even if you should lie among the lots, [you shall have] the wings of a dove covered with silver, and her breast with yellow gold.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 When the heavenly One scatters kings upon it, they shall be made snow-white in Selmon.
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 The mountain of God is a rich mountain; a swelling mountain, a rich mountain.
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 Therefore do you conceive [evil], you swelling mountains? [this is] the mountain which God has delighted to dwell in; yes, the Lord will dwell [in it] for ever.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 The chariots of God are ten thousand fold, thousands of rejoicing ones: the Lord is among them, in Sina, in the holy place.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 You are gone up on high, you have led captivity captive, you have received gifts for man, yes, for [they were] rebellious, that you might dwell among them.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Blessed be the Lord God, blessed be the Lord daily; and the God of our salvation shall prosper us. (Pause)
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Our God is the God of salvation; and to the Lord belong the issues from death.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 But God shall crust the heads of his enemies; the hairy crown of them that go on in their trespasses.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 The Lord said, I will bring again from Basan, I will bring [my people] again through the depths of the sea.
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 That your foot may be dipped in blood, [and] the tongue of your dogs [be stained] with that of [your] enemies.
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 Your goings, O God, have been seen; the goings of my God, the king, in the sanctuary.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 The princes went first, next before the players on instruments, in the midst of damsels playing on timbrels.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 Praise God in the congregations, the Lord from the fountains of Israel.
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 There is Benjamin the younger [one] in ecstasy, the princes of Juda their rulers, the princes of Zabulon, the princes of Nephthali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 O God, command you your strength: strengthen, O God, this which you have wrought in us.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 Because of your temple at Jerusalem shall kings bring presents to you.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Rebuke the wild beasts of the reed: let the crowd of bulls with the heifers of the nations [be rebuked], so that they who have been proved with silver may not be shut out: scatter you the nations that wish for wars.
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 Ambassadors shall arrive out of Egypt; Ethiopia shall hasten [to stretch out] her hand readily to God.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Sing to God, you kingdoms of the earth; sing psalms to the Lord. (Pause)
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 Sing to God that rides on the heaven of heaven, eastward: behold, he will utter a mighty sound with his voice.
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Give you glory to God: his excellency is over Israel, and his power is in the clouds.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 God is wonderful in his holy [places], the God of Israel: he will give power and strength to his people: blessed be God.
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psalms 68 >