< Psalms 49 >

1 For the end, a Psalm for the sons of Core. Hear these words, all you nations, listen, all you that dwell upon the earth:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 both the sons of mean men, and sons of [great] men; the rich and poor [man] together.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 My mouth shall speak of wisdom; and the meditation of my heart shall bring [forth] understanding.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 I will incline mine ear to a parable: I will open my riddle on the harp.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Therefore should I fear in the evil day? the iniquity of my heel shall compass me.
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 They that trust in their strength, and boast themselves in the multitude of their wealth—
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 A brother does not redeem, shall a man redeem? he shall not give to God a ransom for himself,
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 or the price of the redemption of his soul, though he labor for ever,
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 and live to the end, [so] that he should not see corruption.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 When he shall see wise men dying, the fool and the senseless one shall perish together; and they shall leave their wealth to strangers.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 And their sepulchres are their houses for ever, [even] their tabernacles to all generations: they have called their lands after their own names.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 And man being in honor, understands not: he is compared to the senseless cattle, and is like to them.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 This their way is an offense to them: yet afterwards men will commend their sayings. (Pause)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 They have laid [them] as sheep in Hades; death shall feed on them; and the upright shall have dominion over them in the morning, and their help shall fail in Hades from their glory. (Sheol h7585)
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
15 But God shall deliver my soul from the power of Hades, when he shall receive me. (Pause) (Sheol h7585)
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
16 Fear not when a man is enriched, and when the glory of his house is increased.
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 For he shall take nothing when he dies; neither shall his glory descend with him.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 For his soul shall be blessed in his life: he shall give thanks to you when you do well to him.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 [Yet] he shall go in to the generation of his fathers; he shall never see light.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 Man that is in honor, understands not: he is compared to the senseless cattle, and is like them.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.

< Psalms 49 >