< Psalms 37 >

1 [A Psalm] of David. Fret not yourself because of evil-doers, neither be envious of them that do iniquity.
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 For they shall soon be withered as the grass, and shall soon fall away as the green herbs.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Hope in the Lord, and do good; and dwell on the land, and you shall be fed with the wealth of it.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Delight [yourself] in the Lord; and he shall grant you the requests of your heart.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Disclose your way to the Lord, and hope in him; and he shall bring [it] to pass.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 And he shall bring forth your righteousness as the light, and your judgment as the noon-day.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Submit yourself to the Lord, and supplicate him: fret not yourself because of him that prospers in his way, at the man that does unlawful deeds.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 ease from anger, and forsake wrath: fret not yourself so as to do evil.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 For evil-doers shall be destroyed: but they that wait on the Lord, they shall inherit the land.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 And yet a little while, and the sinner shall not be, and you shall seek for his place, and shall not find [it].
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 But the meek shall inherit the earth; and shall delight [themselves] in the abundance of peace.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 The sinner will watch for the righteous, and gnash his teeth upon him.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 But the Lord shall laugh at him: for he foresees that his day will come.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 Sinners have drawn their swords, they have bent their bow, to cast down the poor and needy one, [and] to kill the upright in heart.
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Let their sword enter into their [own] heart, and their bows be broken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 A little is better to the righteous than abundant wealth of sinners.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 For the arms of sinners shall be broken; but the Lord supports the righteous.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 The Lord knows the ways of the perfect; and their inheritance shall be for ever.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 They shall not be ashamed in an evil time; and in days of famine they shall be satisfied.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 For the sinners shall perish; and the enemies of the Lord at the moment of their being honored and exalted have utterly vanished like smoke.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 The sinner borrows, and will not pay again: but the righteous has compassion, and gives.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 For they that bless him shall inherit the earth; and they that curse him shall be utterly destroyed.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 The steps of a man are rightly ordered by the Lord: and he will take pleasure in his way.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 When he falls, he shall not be ruined: for the Lord supports his hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 I was [once] young, indeed I am now old; yet I have not seen the righteous forsaken, nor his seed seeking bread.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 He is merciful, and lends continually; and his seed shall be blessed.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Turn aside from evil, and do good; and dwell for ever.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 For the Lord loves judgment, and will not forsake his saints; they shall be preserved for ever: the blameless shall be avenged, but the seed of the ungodly shall be utterly destroyed.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 But the righteous shall inherit the earth, and dwell upon it for ever.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 The mouth of the righteous will meditate wisdom, and his tongue will speak of judgment.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 The law of his God is in his heart; and his steps shall not slide.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 The sinner watches the righteous, and seeks to kill him.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 But the Lord will not leave him in his hands, nor by any means condemn him when he is judged.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Wait on the Lord, and keep his way, and he shall exalt you to inherit the land: when the wicked are destroyed, you shall see [it].
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 I saw the ungodly very highly exalting himself, and lifting himself up like the cedars of Libanus.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Yet I passed by, and behold! he was not: and I sought him, but his place was not found.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Maintain innocence, and behold uprightness: for there is a remnant to the peaceful man.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 But the transgressors shall be utterly destroyed together: the remnants of the ungodly shall be utterly destroyed.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 But the salvation of the righteous is of the Lord; and he is their defender in the time of affliction.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 And the Lord shall help them, and deliver them: and he shall rescue them from sinners, and save them, because they have hoped in him.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Psalms 37 >