< Numbers 18 >

1 And the Lord spoke to Aaron, saying, You and your sons and your father's house shall bear the sins of the holy things, and you and your sons shall bear the iniquity of your priesthood.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
2 And take to yourself your brethren the tribe of Levi, the family of your father, and let them be joined to you, and let them minister to you; and you and your sons with you [shall minister] before the tabernacle of witness.
Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
3 And they shall keep your charges, and the charges of the tabernacle; only they shall not approach the holy vessels and the altar, so both they and you shall not die.
Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
4 And they shall be joined to you, and shall keep the charges of the tabernacle of witness, in all the services of the tabernacle; and a stranger shall not approach to you.
Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
5 And you shall keep the charges of the holy things, and the charges of the altar, and [so] there shall not be anger among the children of Israel.
“Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
6 And I have taken your brethren the Levites out of the midst of the children of Israel, a present given to the Lord, to minister in the services of the tabernacle of witness.
Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
7 And you and your sons after you shall keep up your priestly ministration, according to the whole manner of the altar, and that which is within the veil; and you shall minister in the services as the office of your priesthood; and the stranger that comes near shall die.
Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
8 And the Lord said to Aaron, And, behold, I have given you the charge of the first fruits of all things consecrated to me by the children of Israel; and I have given them to you as an honor, and to your sons after you for a perpetual ordinance.
Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
9 And let this be to you from all the holy things that are consecrated [to me, even] the burnt offerings, from all their gifts, and from all their sacrifices, and from every trespass-offering of theirs, and from all their sin-offerings, whatever things they give to me of all their holy things, they shall be your and your sons'.
Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
10 In the most holy place shall you eat them; every male shall eat them, you and your sons: they shall be holy to you.
Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
11 And this shall be to you of the first fruits of their gifts, of all the wave-offerings of the children of Israel; to you have I given them and to your sons and your daughters with you, a perpetual ordinance; every clean person in your house shall eat them.
“Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
12 Every first-offering of oil, and every first-offering of wine, their first fruits of corn, whatever they may give to the Lord, to you have I given them.
“Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
13 All the first fruits that are in their land, whatever they shall offer to the Lord, shall be your: every clean person in your house shall eat them.
Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
14 Every devoted thing among the children of Israel shall be your.
“Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
15 And every thing that opens the womb of all flesh, whatever they bring to the Lord, whether man or beast, shall be your: only the firstborn of men shall be surely redeemed, and you shall redeem the firstborn of unclean cattle.
Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
16 And the redemption of them [shall be] from a month old; their valuation of five shekels—it is twenty oboli according to the holy shekel.
Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
17 But you shall not redeem the firstborn of calves and the firstborn of sheep and the firstborn of goats; they are holy: and you shall pour their blood upon the altar, and you shall offer the fat as a burnt offering for a smell of sweet savor to the Lord.
“Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
18 And the flesh shall be your, as also the breast of the wave-offering and as the right shoulder, it shall be your.
Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
19 Every special offering of the holy things, whatever the children of Israel shall specially offer to the Lord, I have given to you and to your sons and to your daughters with you, a perpetual ordinance: it is a covenant of salt for ever before the Lord, for you and your seed after you.
Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
20 And the Lord said to Aaron, You shall have no inheritance in their land, neither shall you have any portion among them; for I [am] your portion and your inheritance in the midst of the children of Israel.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
21 And, behold, I have given to the sons of Levi every tithe in Israel for an inheritance for their services, whenever they perform ministry in the tabernacle of witness.
“Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
22 And the children of Israel shall no more draw near to the tabernacle of witness to incur fatal guilt.
Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
23 And the Levite himself shall perform the service of the tabernacle of witness; and they shall bear their iniquities, it is a perpetual statute throughout their generations; and in the midst of the children of Israel they shall not receive an inheritance.
Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
24 Because I have given as a distinct portion to the Levites for an inheritance the tithes of the children of Israel, whatever they shall offer to the Lord; therefore I said to them, In the midst of the children of Israel they shall have no inheritance.
A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
25 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
26 You shall also speak to the Levites, and shall say to them, If you take the tithe from the children of Israel, which I have given you from them for an inheritance, then shall you separate from it a heave-offering to the Lord, a tenth of the tenth.
“Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
27 And your heave-offerings shall be reckoned to you as corn from the floor, and an offering from the wine-press.
Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
28 So shall you also separate them from all the offerings of the Lord out of all your tithes, whatever you shall receive from the children of Israel; and you shall give of them an offering to the Lord to Aaron the priest.
Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
29 Of all your gifts you shall offer an offering to the Lord, and of every first-fruit the consecrated part from it.
Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
30 And you shall say to them, When you shall offer the first fruits from it, then shall it be reckoned to the Levites as produce from the threshing floor, and as produce from the wine-press.
“Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
31 And you shall eat it in any place, you and your families; for this is your reward for your services in the tabernacle of witness.
Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
32 And you shall not bear sin by reason of it, for you shall have offered an offering of first fruits from it, and you shall not profane the holy things of the children of Israel, that you die not.
Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”

< Numbers 18 >