< Numbers 15 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak to the children of Israel, and you shall say to them, When you are come into the land of your habitation, which I give to you,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
3 and you will offer whole burnt offerings to the Lord, a whole burnt offering or a meat-offering to perform a vow, or a free-will offering, or to offer in your feasts a sacrifice of sweet savor to the Lord, whether of the herd or the flock:
kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
4 then he that offers his gift to the Lord shall bring a meat-offering of fine flour, a tenth part of an ephah mingled with oil, even with the fourth part of a hin.
sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
5 And for a drink-offering you shall offer the fourth part of a hin on the whole burnt offering, or on the meat-offering: for every lamb you shall offer so much, as a sacrifice, a smell of sweet savor to the Lord.
Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
6 And for a ram, when you offer it as a whole burnt offering or as a sacrifice, you shall prepare as a meat-offering two tenths of fine flour mingled with oil, the third part of a hin.
“‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
7 And you shall offer for a smell of sweet savor to the Lord wine for a drink-offering, the third part of a hin.
da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
8 And if you sacrifice [a bullock] from the herd for a whole burnt offering or for a sacrifice, to perform a vow or a peace-offering to the Lord,
“‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
9 then [the worshipper] shall offer upon the calf a meat-offering, three tenth deals of fine flour mingled with oil, [even] the half of a hin.
sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
10 And wine for a drink-offering the half of a hin, a sacrifice for a smell of sweet savor to the Lord.
A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
11 Thus shall you do to one calf or to one ram, or to one lamb of the sheep or kid of the goats.
Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
12 According to the number of what you shall offer, so shall you do to each one, according to their number.
Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
13 Every native of the country shall do thus to offer such things as sacrifices for a smell of sweet savor to the Lord.
“‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 And if there should be a stranger among you in your land, or one who should be born to you among your generations, and he will offer a sacrifice, a smell of sweet savor to the Lord—as you do, so the [whole] congregation shall offer to the Lord.
Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
15 There shall be one law for you and for the strangers dwelling among you, a perpetual law for your generations: as you [are], so shall the stranger be before the Lord.
Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
16 There shall be one law and one ordinance for you, and for the stranger that abides among you.
Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
17 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Speak to the sons of Israel, and you shall say to them, When you are entering into the land, into which I bring you,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
19 then it shall come to pass, when you shall eat of the bread of the land, you shall separate a wave-offering, a special offering to the Lord, the first fruits of your dough.
kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
20 You shall offer your bread a heave-offering: as a heave-offering from the threshing floor, so shall you separate it,
Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
21 even the first fruits of your dough, and you shall give the Lord a heave-offering throughout your generations.
A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
22 But whenever you shall transgress, and not perform all these commands, which the Lord spoke to Moses;
“‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
23 as the Lord appointed you by the hand of Moses, from the day which the Lord appointed you and forward throughout your generations,
ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
24 then it shall come to pass, if a trespass be committed unwillingly, unknown to the congregation, then shall all the congregation offer a calf of the herd without blemish for a whole burnt offering of sweet savor to the Lord, and its meat-offering and its drink-offering according to the ordinance, and one kid of the goats for a sin-offering.
in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
25 And the priest shall make atonement for all the congregation of the children of Israel, and [the trespass] shall be forgiven them, because it is involuntary; and they have brought their gift, a burnt offering to the Lord for their trespass before the Lord, even for their involuntary sins.
Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
26 And it shall be forgiven as respects all the congregation of the children of Israel, and the stranger that is dwelling among you, because [it is] involuntary to all the people.
Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
27 And if one soul sin unwillingly, he shall bring one she-goat of a year old for a sin-offering.
“‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
28 And the priest shall make atonement for the soul that committed the trespass unwillingly, and that sinned unwillingly before the Lord, to make atonement for him.
Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
29 There shall be one law for the native among the children of Israel, and for the stranger that abides among them, whoever shall commit a trespass unwillingly.
Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
30 And whatever soul either of the natives or of the strangers shall do any thing with a presumptuous hand, he will provoke God; that soul shall be cut off from his people,
“‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
31 for he has set at nothing the word of the Lord and broken his commands: that soul shall be utterly destroyed, his sin [is] upon him.
gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
32 And the children of Israel were in the wilderness, and they found a man gathering sticks on the sabbath-day.
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33 And they who found him gathering sticks on the sabbath-day brought him to Moses and Aaron, and to all the congregation of the children of Israel.
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34 And they placed him in custody, for they did not determine what they should do to him.
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35 And the Lord spoke to Moses, saying, Let the man be by all means put to death: [do you] all the congregation, stone him with stones.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36 And all the congregation brought him forth out of the camp; and all the congregation stoned him with stones outside the camp, as the Lord commanded Moses.
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
37 And the Lord spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
38 Speak to the children of Israel, and you shall tell them; and let them make for themselves fringes upon the borders of their garments throughout their generations: and you shall put upon the fringes of the borders a lace of blue.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
39 And it shall be on your fringes, and you shall look on them, and you shall remember all the commands of the Lord, and do them: and you shall not turn back after your imaginations, and after [the sight of your] eyes in the things after which you go a whoring;
Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
40 that you may remember and perform all my commands, and you shall be holy to your God.
Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
41 I [am] the Lord your God that brought you out of the land of Egypt, to be your God: I [am] the Lord your God.
Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Numbers 15 >